< Salmos 69 >
1 Salmo de Davi, para o regente, conforme “os lírios”: Salva-me, ó Deus, porque as águas têm entrado [e encoberto] a minha alma.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 Afundei-me em um profundo lamaçal, onde não se pode ficar em pé; entrei nas profundezas das águas, e a corrente está me levando.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 Já estou cansado de clamar, minha garganta enrouqueceu; meus olhos desfaleceram, enquanto espero pelo meu Deus.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 Os que me odeiam sem motivo são mais numerosos que os cabelos de minha cabeça; são poderosos os que procuram me arruinar, os que por falsidades se fazem meus inimigos; tive que pagar de volta aquilo que não furtei.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 Tu, Deus, sabes como sou tolo; e meus pecados não estão escondidos perante ti.
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 Não sejam envergonhados por minha causa aqueles que te esperam, ó Senhor DEUS dos exércitos; não sejam humilhados por minha causa os que te buscam, ó Deus de Israel.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 Porque por causa de ti aguentei ser insultado; a humilhação cobriu o meu rosto.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 Tornei-me estranho aos meus irmãos; e desconhecido aos filhos de minha mãe;
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 Porque o zelo por tua casa me devorou; e os insultos dos que te insultam caíram sobre mim;
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 Minha alma chorou e jejuou; porém [mais] insultos vieram sobre mim.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 Vesti-me de saco, mas fui ridicularizado por eles num ditado.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 Os que se sentam à porta falam [mal] de mim; e os bebedores de álcool cantam [piadas] contra mim.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 Mas eu oro a ti, SENHOR, [no] tempo aceitável. Pela grandeza de tua bondade, responde-me, ó Deus, pela fidelidade de tua salvação.
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Livra-me do lamaçal, e não me deixes afundar; seja eu resgatado dos que me odeiam, e das profundezas das águas.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 Não permitas que as correntes de águas me cubram, e que a profundeza não me devore, nem o poço feche sua boca sobre mim.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Responde-me, SENHOR; pois boa é tua bondade; olha para mim conforme tua piedade.
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 E não escondas teu rosto de teu servo; porque estou angustiado; ouve-me depressa.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Vem para perto de minha alma, [e] a liberta; resgata-me por causa de meus inimigos.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 Tu conheces como me insultam, me envergonham e me humilham; diante de ti estão todos os meus adversários.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 Insultos têm quebrado meu coração, e estou fraquíssimo; e esperei compaixão, porém [houve] nenhuma; [também esperei] por pessoas que me consolassem, mas não os achei.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 Deram-me fel como alimento; e em minha sede me deram vinagre para beber.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 Torne-se a mesa diante deles como que um laço; e aquilo que [lhes] dá segurança [lhes] seja uma armadilha.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Sejam escurecidos os olhos deles, para que não possam ver; e que seus quadris vacilem continuamente.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Derrama tua indignação sobre eles; e que sejam tomados pelo ardor de tua ira.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 A habitação deles seja desolada; e que não haja morador nas tendas deles;
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 Porque perseguem [aquele] a quem tu feriste, e contam histórias da dor daqueles a quem tu machucaste.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Conta como maldade a maldade deles; e não sejam eles agraciados por tua justiça.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 Sejam riscados dos livro da vida; e não estejam eles escritos junto com os justos.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 Mas eu [estou] miserável e em dores; ó Deus, que tua salvação me proteja.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 Louvarei o nome de Deus com cântico; e o engrandecerei com agradecimentos.
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 Isto agradará ao SENHOR mais do que [o sacrifício] de um boi [ou] de um bezerro com chifres e unhas.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 Os mansos verão, e se alegrarão; vós que buscais a Deus, vosso coração viverá.
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 Porque o SENHOR ouve aos necessitados, e não despreza os prisioneiros que lhe pertencem.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 Louvem a ele os céus, a terra, os mares, e tudo que neles se move;
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 Porque Deus salvará a Sião, e construirá as cidades de Judá; e habitarão ali, e a terão como posse.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 E a semente de seus servos a herdará; e os que amam o nome dele habitarão nela.
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.