< Salmos 66 >
1 Cântico e salmo para o regente: Gritai de alegria a Deus toda a terra.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Cantai a glória do nome dele; reconhecei a glória de seu louvor.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Dizei a Deus: Tu [és] temível [em] tuas obras; pela grandeza de tua força os teus inimigos se sujeitarão a ti.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Toda a terra te adorará, e cantará a ti; cantarão ao teu nome. (Selá)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Vinde, e vede os atos de Deus; a obra dele é temível aos filhos dos homens.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Ele fez o mar ficar seco, passaram o rio a pé; ali nos alegramos nele.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Ele governa com seu poder para sempre; seus olhos vigiam as nações; não se exaltem os rebeldes. (Selá)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Vós povos, bendizei a nosso Deus, e fazei ouvir a voz do louvor a ele,
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 Que conserva nossas almas em vida, e não permite que nossos pés se abalem.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Porque tu, Deus, tem nos provado; tu nos refinas como se refina a prata.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Tu nos levaste a uma rede; prendeste-nos em nossas cinturas.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Fizeste um homem cavalgar sobre nossas cabeças; passamos pelo fogo e pela água, porém tu nos tiraste para um [lugar] confortável.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Entrarei em tua casa com holocaustos; pagarei a ti os meus votos,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Que meus lábios pronunciaram, e minha boca falou, quando eu estava angustiado.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Eu te oferecerei holocaustos de animais gordos, com incenso de carneiros; prepararei bois com bodes. (Selá)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Vinde, ouvi, todos vós que temeis a Deus, e eu contarei o que ele fez à minha alma.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Clamei a ele com minha boca, e ele foi exaltado pela minha língua.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Se eu tivesse dado valor para a maldade em meu coração, o Senhor não teria [me] ouvido.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 Mas certamente Deus [me] ouviu; ele prestou atenção à voz de minha oração.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Bendito seja Deus, que não ignorou minha oração, nem sua bondade [se desviou] de mim.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!