< Salmos 50 >

1 Salmo de Asafe: Deus, o SENHOR Deus fala e chama a terra, desde onde o sol nasce até onde ele se põe.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 Desde Sião, a perfeição da beleza, Deus mostra seu imenso brilho.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Nosso Deus virá, e não ficará calado; fogo queimará adiante dele, e ao redor dele haverá grande tormenta.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Ele chamará aos céus do alto, e à terra, para julgar a seu povo.
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 Ajuntai-me meus santos, que confirmam meu pacto por meio de sacrifício.
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 E os céus anunciarão sua justiça, pois o próprio Deus é o juiz. (Selá)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 Ouve, povo meu, e eu falarei; eu darei testemunho contra ti, Israel; eu sou Deus, o teu Deus.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Eu não te repreenderei por causa de teus sacrifícios, porque teus holocaustos estão continuamente perante mim.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 Não tomarei bezerro de tua casa, [nem] bodes de teus currais;
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 Porque todo animal das matas é meu, [e também] os milhares de animais selvagens das montanhas.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Conheço todas as aves das montanhas, e as feras do campo [estão] comigo.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Se eu tivesse fome, não te diria, porque meu é o mundo, e tudo o que nele há.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Comeria eu carne de touros, ou beberia sangue de bodes?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Oferece a Deus sacrifício de louvor, e paga ao Altíssimo os teus votos.
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 E clama a mim no dia da angústia; e eu te farei livre, e tu me glorificarás.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Mas Deus diz ao perverso: Para que tu recitas meus estatutos, e pões meu pacto em tua boca?
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Pois tu odeias a repreensão, e lança minhas palavras para detrás de ti.
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Se vês ao ladrão, tu consentes com ele; e tens tua parte com os adúlteros.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Com tua boca pronuncias o mal, e tua língua gera falsidades.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Tu te sentas [e] falas contra teu irmão; contra o filho de tua mãe tu dizes ofensas.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Tu fazes estas coisas, e eu fico calado; pensavas que eu seria como tu? Eu te condenarei, e mostrarei [teus males] diante de teus olhos.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Entendei, pois, isto, vós que vos esqueceis de Deus; para que eu não [vos] faça em pedaços, e não haja quem [vos] livre.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Quem oferece sacrifício de louvor me glorificará, e ao que cuida de seu caminho, eu lhe mostrarei a salvação de Deus.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Salmos 50 >