< Salmos 26 >
1 Salmo de Davi: Faze-me justiça, SENHOR, pois eu ando em minha sinceridade; e eu confio no SENHOR, não me abalarei.
Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
2 Prova-me, SENHOR, e testa-me; examina meus sentimentos e meu coração.
Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
3 Porque tua bondade está diante dos meus olhos; e eu ando em tua verdade.
gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
4 Não me sento com homens vãos, nem converso com desonestos.
Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
5 Eu odeio a reunião dos malfeitores; e não me sento com os perversos.
na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
6 Lavo minhas mãos em inocência, e ando ao redor do teu altar, SENHOR;
Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
7 Para que eu declare com voz de louvores, e para contar todas as tuas maravilhas.
ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
8 SENHOR, eu amo a morada de tua Casa, e o lugar onde habita a tua glória.
Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
9 Não juntes minha alma com os pecadores, nem minha vida com homens sanguinários;
Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
10 Nas mãos deles há más intenções; e sua mão direita é cheia de suborno.
waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
11 Mas eu ando em minha sinceridade; livra-me e tem piedade de mim.
Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
12 Meu pé está em um caminho plano; louvarei ao SENHOR nas congregações.
Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.