< Salmos 21 >
1 Salmo de Davi para o regente: SENHOR, em tua força o rei se alegra; e como ele fica contente com tua salvação!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
2 Tu lhe deste o desejo de seu coração; e tu não negaste o pedido de seus lábios. (Selá)
Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
3 Porque tu foste até ele com bênçãos de bens; tu puseste na cabeça dele uma coroa de ouro fino.
Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
4 Ele te pediu vida, [e] tu lhe deste; muitos dias, para todo o sempre.
Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
5 Grande [é] a honra dele por tua salvação; honra e majestade tu lhe concedeste.
Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
6 Porque tu o pões em bênçãos para sempre; tu fazes abundante a alegria dele com tua face.
Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
7 Porque o rei confia no SENHOR; e ele nunca se abalará com a bondade do Altíssimo.
Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
8 Tua mão alcançará a todos o os teus inimigos; tua mão direita encontrará aos que te odeiam.
Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
9 Tu os porás como que [num] forno de fogo no tempo [em que se encontrarem] em tua presença; o SENHOR em sua ira os devorará; e fogo os consumirá.
A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
10 Tu destruirás o fruto deles de [sobre] a terra; e [também] a semente deles dos filhos dos homens.
Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
11 Porque eles quiseram o mal contra ti; planejaram uma cilada, [mas] não tiveram sucesso.
Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
12 Porque tu os porás em fuga; com [tuas flechas] nas cordas tu lhes apontarás no rosto.
gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
13 Exalta-te, SENHOR, em tua força; cantaremos e louvaremos o teu poder.
Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.