< Salmos 145 >

1 Cântico de Davi: Eu te exaltarei, meu Deus [e] Rei; e bendirei teu nome para todo o sempre.
Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
2 Todo dia eu te bendirei, e louvarei teu nome para todo o sempre.
Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
3 O SENHOR é grande e muito louvável; sua grandeza é incompreensível.
Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
4 Geração após geração louvará tuas obras, e anunciarão tuas proezas.
Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
5 Eu falarei da honra gloriosa de tua majestade, e de teus feitos maravilhosos.
Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
6 E falarão do poder de teus assombrosos feitos; e eu contarei tua grandeza.
Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
7 Declararão a lembrança de tua grande bondade; e anunciarão tua justiça alegremente.
Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
8 Piedoso e misericordioso é o SENHOR; ele demora para se irar, e tem grande bondade.
Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
9 O SENHOR é bom para com todos; e suas misericórdias [estão] sobre todas as obras que ele fez.
Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
10 Todas as tuas obras louvarão a ti, SENHOR; e teus santos te bendirão.
Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
11 Contarão a glória de teu reino, e falarão de teu poder.
Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
12 Para anunciarem aos filhos dos homens suas proezas, e a honra gloriosa de seu reino.
saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
13 Teu reino é um reino eterno, e teu domínio [dura] geração após geração.
Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
14 O SENHOR segura todos os que caem, e levanta todos os abatidos.
Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
15 Os olhos de todos esperam por ti, e tu lhes dás seu alimento ao seu tempo.
Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
16 Tu abres tua mão, e sacias o desejo de todo ser vivo.
Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
17 O SENHOR [é] justo em todos os seus caminhos, e bondoso em todas as suas obras.
Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
18 O SENHOR está perto de todos os que o chamam; de todos os que clamam a ele sinceramente.
Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
19 Ele faz a vontade dos que o temem; e ouve o clamor deles, e os salva.
Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
20 O SENHOR protege a todos os que o amam; porém destrói a todos os perversos.
Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
21 Minha boca anunciará louvores ao SENHOR; e todo [ser feito de] carne louvará seu santo nome para todo o sempre.
Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.

< Salmos 145 >