< Salmos 12 >

1 Salmo de Davi, para o regente, com harpa de oito cordas: Salva, SENHOR, porque os bons estão em falta; porque são poucos os fiéis dentre os filhos dos homens.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
2 Cada um fala falsidade ao seu próximo, [com] lábios elogiam falsamente; falam com duas intenções no coração.
Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
3 Que o SENHOR corte a todos os lábios que falam falsos elogios, [e toda] língua que fala grandes [mentiras].
Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
4 Pois dizem: Com nossa língua prevaleceremos; nossos lábios [são] nossos; que é senhor sobre nós?
masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
5 O SENHOR diz: Pela opressão aos humildes, pelo gemido dos necessitados, eu agora me levantarei; porei em segurança àquele a quem ele sopra [desejando oprimir].
“Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
6 As palavras do SENHOR são palavras puras, [como] prata refinada em forno de barro, purificada sete vezes.
Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
7 Tu, SENHOR, os guardarás; desta geração os livrarás para sempre.
Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
8 Os maus andam cercando, enquanto os mais vis dos filhos dos homens são exaltados.
Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.

< Salmos 12 >