< Salmos 119 >

1 [Álefe]: Bem-aventurados são os puros em [seus] caminhos, os que andam na lei do SENHOR.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Bem-aventurados são os que guardam os testemunhos dele, [e] o buscam com todo o coração;
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 E não praticam perversidade, [mas] andam nos caminhos dele.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tu mandaste que teus mandamentos fossem cuidadosamente obedecidos.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 Ah! Como gostaria que meus caminhos fossem dirigidos a guardar teus estatutos!
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Então não me envergonharia, quando eu observasse todos os teus mandamentos.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Louvarei a ti com um coração correto, enquanto aprendo os juízos de tua justiça.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Eu guardarei teus estatutos; não me abandones por completo.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 [Bete]: Com que um rapaz purificará o seu caminho? Sendo obediente conforme a tua palavra.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Eu te busco como todo o meu coração; não me deixes desviar de teus mandamentos.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 Guardei a tua palavra em meu coração, para eu não pecar contra ti.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Bendito [és] tu, SENHOR; ensina-me os teus estatutos.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Com meus lábios contei todos os juízos de tua boca.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Eu me alegro mais com o caminho de teus estatutos, do que com todas as riquezas.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Meditarei em teus mandamentos, e darei atenção aos teus caminhos.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Terei prazer em teus estatutos; não me esquecerei de tua palavra.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 [Guímel]: Trata bem o teu servo, [para] que eu viva, e obedeça tua palavra.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Abre meus olhos, para que eu veja as maravilhas de tua lei.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Eu sou peregrino na terra, não escondas de mim os teus mandamentos.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Minha alma está despedaçada de tanto desejar os teus juízos em todo tempo.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Tu repreendes aos malditos arrogantes, que se desviam de teus mandamentos.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Tira-me de minha humilhação e desprezo, pois eu guardei teus testemunhos.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Até mesmo os príncipes se sentaram, e falaram contra mim; porém o teu servo estava meditando em teus estatutos.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Pois teus testemunhos são meus prazeres [e] meus conselheiros.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 [Dálete]: Minha alma está grudada ao pó; vivifica-me conforme tua palavra.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Eu [te] contei os meus caminhos, e tu me respondeste; ensina-me conforme teus estatutos.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Faze-me entender o caminho de teus preceitos, para eu falar de tuas maravilhas.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Minha alma se derrama de tristeza; levanta-me conforme tua palavra.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Desvia de mim o caminho de falsidade; e sê piedoso dando-me tua lei.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 Eu escolhi o caminho da fidelidade; e pus [diante de mim] os teus juízos.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Estou apegado a teus testemunhos; ó SENHOR, não me envergonhes.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Correrei pelo caminho de teus mandamentos, porque tu alargaste o meu coração.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 [Hê]: Ensina-me, SENHOR, o caminho de teus estatutos, e eu o guardarei até o fim.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Dá-me entendimento, e eu guardarei a tua lei, e a obedecerei de todo [o meu] coração.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Faze-me andar na trilha de teus mandamentos, porque nela tenho prazer.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Inclina meu coração a teus testemunhos, e não à ganância.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Desvia meus olhos para que não olhem para coisas inúteis; vivifica-me pelo teu caminho.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Confirma tua promessa a teu servo, que tem temor a ti.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Desvia de mim a humilhação que eu tenho medo, pois teus juízos são bons.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Eis que amo os teus mandamentos; vivifica-me por tua justiça.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 [Vau]: E venham sobre mim tuas bondades, SENHOR; [e também] a tua salvação, segundo tua promessa.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 Para que eu tenha resposta ao que me insulta; pois eu confio em tua palavra.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 E nunca tires de minha boca a palavra da verdade, pois eu espero em teus juízos.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Assim obedecerei a tua lei continuamente, para todo o sempre.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 E andarei [livremente] por longas distâncias, pois busquei teus preceitos.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Também falarei de teus testemunhos perante reis, e não me envergonharei.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 E terei prazer em teus mandamentos, que eu amo.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 E levantarei as minhas mãos a teus mandamentos, que eu amo; e meditarei em teus estatutos.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 [Záin]: Lembra-te da palavra [dada] a teu servo, à qual mantenho esperança.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 Isto é meu consolo na minha aflição, porque tua promessa me vivifica.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Os arrogantes têm zombado de mim demasiadamente; [porém] não me desviei de tua lei.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Eu me lembrei de teus juízos muito antigos, SENHOR; e [assim] me consolei.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 Eu me enchi de ira por causa dos perversos, que abandonam tua lei.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Teus estatutos foram meus cânticos no lugar de minhas peregrinações.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 De noite tenho me lembrado de teu nome, SENHOR; e tenho guardado tua lei.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Isto eu tenho feito, porque guardo teus mandamentos.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 [Hete]: O SENHOR é minha porção; eu disse que guardaria tuas palavras.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Busquei a tua face com todo o [meu] coração; tem piedade de mim segundo tua palavra.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 Eu dei atenção a meus caminhos, e dirigi meus pés a teus testemunhos.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Eu me apressei, e não demorei a guardar os teus mandamentos.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Bandos de perversos me roubaram; [porém] não me esqueci de tua lei.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 No meio da noite eu me levanto para te louvar, por causa dos juízos de tua justiça.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Sou companheiro de todos os que te temem, e dos que guardam os teus mandamentos.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 A terra está cheia de tua bondade, SENHOR; ensina-me os teus estatutos.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 [Tete]: Tu fizeste bem a teu servo, SENHOR, conforme tua palavra.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Ensina-me bom senso e conhecimento, pois tenho crido em teus mandamentos.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Antes de ter sido afligido, eu andava errado; mas agora guardo tua palavra.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Tu és bom, e fazes o bem; ensina-me os teus estatutos.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Os arrogantes forjaram mentiras contra mim; [mas] eu com todo o [meu] coração guardo os teus mandamentos.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 O coração deles se incha como gordura; [mas] eu tenho prazer em tua lei.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Foi bom pra mim ter sido afligido, para assim eu aprender os teus estatutos.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 Melhor para mim é a lei de tua boca, do que milhares de [peças] de ouro ou prata.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 [Iode]: Tuas mãos me fizeram e me formaram; faze-me ter entendimento, para que eu aprenda teus mandamentos.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Os que te temem olham para mim e se alegram, porque eu mantive esperança em tua palavra.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 Eu sei, SENHOR, que teus juízos são justos; e que tu me afligiste [por] tua fidelidade.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Seja agora tua bondade para me consolar, segundo a promessa [que fizeste] a teu servo.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Venham tuas misericórdias sobre mim, para que eu viva; pois tua lei é o meu prazer.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Sejam envergonhados os arrogantes, porque eles me prejudicaram com mentiras; [porém] eu medito em teus mandamentos.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Virem-se a mim os que te temem e conhecem os teus testemunhos.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Seja meu coração correto em teus estatutos, para eu não ser envergonhado.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 [Cafe]: Minha alma desfalece por tua salvação; em tua palavra mantenho esperança.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Meus olhos desfaleceram por tua promessa, enquanto eu dizia: Quando tu me consolarás?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Porque fiquei como um odre na fumaça, [porém] não me esqueci teus testemunhos.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 Quantos serão os dias de teu servo? Quando farás julgamento aos meus perseguidores?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Os arrogantes me cavaram covas, aqueles que não são conforme a tua lei.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Todos os teus mandamentos são verdade; com mentiras me perseguem; ajuda-me.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Estou quase que destruído por completo sobre a terra; porém eu não deixei teus mandamentos.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Vivifica-me conforme tua bondade, então guardarei o testemunho de tua boca.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 [Lâmede]: Para sempre, SENHOR, tua palavra permanece nos céus.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Tua fidelidade [dura] de geração em geração; tu firmaste a terra, e [assim] ela permanece.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 Elas continuam por tuas ordens até hoje, porque todos são teus servos.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Se a tua lei não fosse meu prazer, eu já teria perecido em minha aflição.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Nunca esquecerei de teus mandamentos, porque tu me vivificaste por eles.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Eu sou teu, salva-me, porque busquei teus preceitos.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Os perversos me esperaram, para me destruírem; [porém] eu dou atenção a teus testemunhos.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 A toda perfeição eu vi fim; [mas] teu mandamento é extremamente grande.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 [Mem]: Ah, como eu amo a tua lei! O dia todo eu medito nela.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Ela me faz mais sábio do que meus inimigos [por meio de] teus mandamentos, porque ela está sempre comigo.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 Sou mais inteligente que todos os meus instrutores, porque medito em teus testemunhos.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Sou mais prudente que os anciãos, porque guardei teus mandamentos.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 Afastei meus pés de todo mau caminho, para guardar tua palavra.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 Não me desviei de teus juízos, porque tu me ensinaste.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 Como são doces tuas palavras ao meu paladar! Mais que o mel em minha boca.
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Obtenho conhecimento por meio de teus preceitos; por isso odeio todo caminho de mentira.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 [Nun]: Tua palavra é lâmpada para meus pés e luz para meu caminho.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 Eu jurei, e [assim] cumprirei, de guardar os juízos de tua justiça.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Eu estou muito aflito, SENHOR; vivifica-me conforme a tua palavra.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Agrada-te das ofertas voluntárias de minha boca, SENHOR; e ensina-me teus juízos.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Continuamente arrisco minha alma, porém não me esqueço de tua lei.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Os perversos me armaram um laço de armadilha, mas não me desviei de teus mandamentos.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Tomei teus testemunhos por herança para sempre, pois eles são a alegria de meu coração.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 Inclinei meu coração para praticar os teus testemunhos para todo o sempre.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 [Sâmeque]: Odeio os inconstantes, mas amo a tua lei.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Tu és meu refúgio e meu escudo; eu espero em tua palavra.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Afastai-vos de mim, malfeitores, para que eu guarde os mandamentos de meu Deus.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Sustenta-me conforme a tua promessa, para que eu viva; e não me faças ser humilhado em minha esperança.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Segura-me, e estarei protegido; então continuamente pensarei em teus estatutos.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Tu atropelas a todos que se desviam de teus estatutos; pois o engano deles é mentira.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Tu tiras a todos os perversos da terra como [se fossem] lixo; por isso eu amo teus testemunhos.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Meu corpo se arrepia de medo de ti; e temo os teus juízos.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 [Áin]: Eu fiz juízo e justiça; não me abandones com os meus opressores.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Sê tu a garantia do bem de teu servo; não me deixes ser oprimido pelos arrogantes.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Meus olhos desfaleceram [de esperar] por tua salvação, e pela palavra de tua justiça.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Age para com teu servo segundo tua bondade, e ensina-me teus estatutos.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Eu sou teu servo. Dá-me entendimento; então conhecerei teus testemunhos.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 É tempo do SENHOR agir, porque estão violando tua lei.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 Por isso eu amo teus mandamentos mais que o ouro, o mais fino ouro.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Por isso considero corretos todos os [teus] mandamentos quanto a tudo, e odeio todo caminho de falsidade.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 [Pê]: Maravilhosos são teus testemunhos, por isso minha alma os guarda.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 A entrada de tuas palavras dá luz, dando entendimento aos simples.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 Abri minha boca, e respirei; porque desejei teus mandamentos.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Olha-me, e tem piedade de mim; conforme [teu] costume para com os que amam o teu nome.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Firma meus passos em tua palavra, e que nenhuma perversidade me domine.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Resgata-me da opressão dos homens; então guardarei teus mandamentos.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Brilha teu rosto sobre teu servo, e ensina-me teus estatutos.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Ribeiros d'água descem de meus olhos, porque eles não guardam tua lei.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 [Tsadê]: Tu és justo, SENHOR; e corretos são teus juízos.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Tu ensinaste teus testemunhos justos e muito fiéis.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Meu zelo me consumiu, porque meus adversários se esqueceram de tuas palavras.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Refinada é a tua palavra, e teu servo a ama.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Eu sou pequeno e desprezado; [porém] não me esqueço de teus mandamentos.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Tua justiça é justa para sempre, e tua lei é verdade.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Aperto e angústia me encontraram; [ainda assim] teus mandamentos são meus prazeres.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 A justiça de teus testemunhos [dura] para sempre; dá-me entendimento, e então viverei.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 [Cofe]: Clamei com todo o [meu] coração; responde-me, SENHOR; guardarei teus estatutos.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 Clamei a ti; salva-me, e então guardarei os teus testemunhos.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Eu me antecedi ao amanhecer, e gritei; [e] mantive esperança em tua palavra.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Meus olhos antecederam as vigílias da noite, para meditar em tua palavra.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Ouve minha voz, segundo tua bondade, SENHOR; vivifica-me conforme teu juízo.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Aproximam-se [de mim] os que praticam maldade; eles estão longe de tua lei.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 [Porém] tu, SENHOR, estás perto [de mim]; e todos os teus mandamentos são verdade.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Desde antigamente eu soube de teus testemunhos, que tu os fundaste para sempre.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 [Rexe]: Olha a minha aflição, e livra-me [dela]; pois não me esqueci de tua lei.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Defende minha causa, e resgata-me; vivifica-me conforme tua palavra.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 A salvação está longe dos perversos, porque eles não buscam teus estatutos.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Muitas são tuas misericórdias, SENHOR; vivifica-me conforme teus juízos.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Muitos são meus perseguidores e meus adversários; [porém] eu não me desvio de teus testemunhos.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 Eu vi aos enganadores e os detestei, porque eles não guardam tua palavra.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Vê, SENHOR, que eu amo teus mandamentos; vivifica-me conforme a tua bondade.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 O princípio de tua palavra é fiel, e o juízo de tua justiça [dura] para sempre.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 [Xin]: Príncipes me perseguiram sem causa, mas meu coração temeu a tua palavra.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Eu me alegro em tua palavra, tal como alguém que encontra um grande tesouro.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Odeio e abomino a falsidade; [mas] amo a tua lei.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Louvo a ti sete vezes ao dia, por causa dos juízos de tua justiça.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Muita paz têm aqueles que amam a tua lei; e para eles não há tropeço.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Espero por tua salvação, SENHOR; e pratico teus mandamentos.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Minha alma guarda teus testemunhos, e eu os amo muito.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 Eu guardo teus preceitos e teus testemunhos, porque todos os meus caminhos estão diante de ti.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 [Tau]: Chegue meu clamor perante teu rosto, SENHOR; dá-me entendimento conforme tua palavra.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Venha minha súplica diante de ti; livra-me conforme tua promessa.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Meus lábios falarão muitos louvores, pois tu me ensinas teus estatutos.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Minha língua falará de tua palavra, porque todos os teus mandamentos são justiça.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Que tua mão me socorra, porque escolhi [seguir] teus preceitos.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 Desejo tua salvação, SENHOR; e tua lei é o meu prazer.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Que minha alma viva e louve a ti; e que teus juízos me socorram.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 Tenho andado sem rumo, como uma ovelha perdida; busca a teu servo, pois eu não me esqueci de teus mandamentos.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.

< Salmos 119 >