< Salmos 105 >

1 Agradecei ao SENHOR, chamai o seu nome; anunciai suas obras entre os povos.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Cantai a ele, tocai músicas para ele; falai de todas as suas maravilhas.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Tende orgulho de seu santo nome; alegre-se o coração dos que buscam ao SENHOR.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Buscai ao SENHOR e à sua força; buscai a presença dele continuamente.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Lembrai-vos de suas maravilhas, que ele fez; de seus milagres, e dos juízos de sua boca.
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 Vós, [que sois da] semente de seu servo Abraão; vós, filhos de Jacó, seus escolhidos.
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Ele é o SENHOR, nosso Deus; seus juízos [estão] em toda a terra.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Ele se lembra para sempre de seu pacto, da palavra que ele mandou até mil gerações;
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 O qual ele firmou com Abraão, e de seu juramento a Isaque.
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 O qual também confirmou a Jacó como estatuto, a Israel como pacto eterno.
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 Dizendo: A ti darei a terra de Canaã, a porção de vossa herança.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Sendo eles poucos em número; [eram] poucos, e estrangeiros nela.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 E andaram de nação em nação, de um reino a outro povo.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Ele não permitiu a ninguém que os oprimisse; e por causa deles repreendeu a reis,
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 [Dizendo]: Não toqueis nos meus ungidos, e não façais mal a meus profetas.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 E chamou a fome sobre a terra; ele interrompeu toda fonte de alimento;
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Enviou um homem adiante deles: José, [que] foi vendido como escravo.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 Amarraram seus pés em correntes; ele foi preso com ferros;
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Até o tempo que sua mensagem chegou, a palavra do SENHOR provou o valor que ele tinha.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 O rei mandou que ele fosse solto; o governante de povos o libertou.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 Ele o pôs como senhor de sua casa, e por chefe de todos os seus bens,
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 Para dar ordens a suas autoridades, e instruir a seus anciãos.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Então Israel entrou no Egito; Jacó peregrinou na terra de Cam.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 E fez seu povo crescer muito, e o fez mais poderoso que seus adversários.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 E mudou o coração [dos outros], para que odiassem ao seu povo, para que tratassem mal a seus servos.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 [Então] enviou seu servo Moisés, e a Arão, a quem tinha escolhido;
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 [Que] fizeram entre eles os sinais anunciados, e coisas sobrenaturais na terra de Cam.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Ele mandou trevas, e fez escurecer; e não foram rebeldes a sua palavra.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Ele transformou suas águas em sangue, e matou a seus peixes.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 A terra deles produziu rãs em abundância, [até] nos quartos de seus reis.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Ele falou, e vieram vários bichos [e] piolhos em todos os seus limites.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 Tornou suas chuvas em saraiva; [pôs] fogo ardente em sua terra.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 E feriu suas vinhas e seus figueirais; e quebrou as árvores de seus territórios.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Ele falou, e vieram gafanhotos, e incontáveis pulgões;
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 E comeram toda a erva de sua terra; e devoraram o fruto de seus campos.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Também feriu a todos os primogênitos em sua terra; os primeiros de todas as suas forças.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 E os tirou [dali] com prata e ouro; e dentre suas tribos não houve quem tropeçasse.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 [Até] o Egito se alegrou com a saída deles, porque seu temor tinha caído sobre eles.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Ele estendeu uma nuvem como cobertor, e um fogo para iluminar a noite.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 Eles pediram, e fez vir codornizes; e os fartou com pão do céu.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Ele abriu uma rocha, e dela saíram águas; [e] correram [como] um rio pelos lugares secos;
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Porque se lembrou de sua santa palavra, e de seu servo Abraão.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 Então ele tirou [dali] a seu povo com alegria; e seus eleitos com celebração.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 E lhes deu as terras das nações; e do trabalho das nações tomaram posse;
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 Para que guardassem seus estatutos, e obedecessem a leis dele. Aleluia!
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Salmos 105 >