< Lucas 1 >
1 Como muitos empreenderam pôr em ordem o relato das coisas que entre nós se cumpriram,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 conforme os que [as] viram que desde o princípio, e foram servidores das palavra, nos transmitiram,
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 pareceu-me bom que também eu, que tenho me informado com exatidão desde o princípio, escrevesse-as em ordem a ti, caríssimo Teófilo,
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 para que conheças a certeza das coisas de que foste ensinado.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 Houve nos dias de Herodes, rei da Judeia, um sacerdote chamado Zacarias, da ordem de Abias; sua mulher das filhas de Arão, e o seu nome era Isabel.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 E ambos eram justos diante de Deus; andavam sem repreensão em todos os mandamentos e preceitos do Senhor.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 Mas não tinham filho, porque Isabel era estéril, e ambos tinham idade avançada.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 E aconteceu que, quando ele fazia o trabalho sacerdotal diante de Deus, na ordem da sua turma,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 conforme o costume do sacerdócio, foi sorteado a entrar no santuário do Senhor para oferecer o incenso.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 E toda a multidão do povo estava fora orando, à hora do incenso.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 Então um anjo do Senhor lhe apareceu em pé, à direita do altar do incenso.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 Quando Zacarias [o] viu, perturbou-se, e o medo o tomou.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 Mas o anjo lhe disse: Zacarias, não temas, pois a tua oração foi ouvida. E Isabel, tua mulher, dará à luz um filho, e lhe porás o nome de João.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 E terás prazer e alegria, e muitos se alegrarão do seu nascimento;
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 pois ele será grande diante do Senhor, e não beberá vinho nem bebida alcoólica, e será cheio do Espírito Santo, já desde o ventre da sua mãe.
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 E converterá muitos dos filhos de Israel ao Senhor seu Deus.
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 E irá adiante dele no espírito e virtude de Elias, para converter os corações dos pais aos filhos, e os rebeldes à prudência dos justos; a fim de preparar um povo pronto ao Senhor.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 Então Zacarias disse ao anjo: Como terei certeza disso? Pois sou velho, e a minha mulher de idade avançada.
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 O anjo lhe respondeu: Eu sou Gabriel, que fico presente diante de Deus, e fui enviado para te falar e te dar estas boas notícias.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 Eis que ficarás mudo, e não poderás falar até o dia em que essas coisas aconteçam, porque não creste nas minhas palavras, que se cumprirão no devido tempo.
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 E o povo estava esperando Zacarias, e se surpreenderam de que ele demorava no santuário.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 Quando ele saiu, não conseguia lhes falar; e entenderam que havia tido alguma visão no santuário. Ele lhes fazia gestos, e continuou mudo.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 E sucedeu que, terminados os dias do seu serviço, voltou à sua casa.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 E depois daqueles dias Isabel, sua mulher, Isabel, engravidou-se, e por cinco meses se escondeu, dizendo:
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 Pois isto o Senhor me fez nos dias em que ele [me] observou, para acabar a minha humilhação entre as pessoas.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 E no sexto mês o anjo Gabriel foi enviado da parte de Deus a uma cidade da Galileia, chamada Nazaré,
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 a uma virgem prometida em casamento com um homem chamado José, da descendência de Davi; e o nome da virgem era Maria.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 O anjo entrou onde ela estava, e disse: Alegra-te, agraciada; o Senhor [é] contigo.
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 Ela perturbou-se muito por essas palavras, e se perguntava que saudação seria esta.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 Então o anjo lhe disse: Maria, não temas, porque encontraste graça diante de Deus.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 E eis que em teu ventre conceberás, darás à luz um filho, e chamarás o seu nome de Jesus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 Ele será grande, e será chamado Filho do Altíssimo; e o Senhor Deus lhe dará o trono de Davi, seu ancestral.
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 E reinará eternamente na casa de Jacó; o seu reino não terá fim. (aiōn )
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
34 Maria disse ao anjo: Como será isso? Pois não conheço intimamente homem algum.
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 O anjo lhe respondeu: O Espírito Santo virá sobre ti, e o poder do Altíssimo te cobrirá com a sua sombra. Por isso o Santo que nascerá será chamado Filho de Deus.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 E eis que Isabel, tua prima, também está grávida de um filho na sua velhice; e este é o sexto mês para a que era chamada de estéril.
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 Pois para Deus nada será impossível.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 Então Maria disse: Eis aqui a serva do Senhor; cumpra-se em mim conforme a tua palavra. E o anjo ausentou-se dela.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 E naqueles dias, Maria levantou-se, e foi apressada à região montanhosa, a uma cidade de Judá.
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 Ela entrou na casa de Zacarias, e cumprimentou Isabel.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 E aconteceu que, quando Isabel ouviu o cumprimento de Maria, a criança saltou no seu ventre, e Isabel foi cheia do Espírito Santo.
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 Então exclamou em alta voz: Bendita [és] tu entre as mulheres, e bendito [é] o fruto do teu ventre!
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 Como me acontece isto, que a mãe de meu Senhor venha a mim?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 Pois eis que, quando a voz do teu cumprimento chegou aos meus ouvidos, a criança saltou de alegria no meu ventre.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 E bendita é a que creu, pois as coisas que da parte do Senhor lhe foram ditas se cumprirão.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 Então Maria disse: A minha alma engrandece ao Senhor,
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 e o meu espírito se alegra em Deus meu Salvador.
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 Porque ele observou a humilde condição da sua serva; pois eis que desde agora todas as gerações me chamarão bendita.
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 Pois o Poderoso me fez grandes coisas; e santo [é] o seu nome.
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 E a sua misericórdia é de geração em geração sobre os que o temem.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 Com o seu braço manifestou poder; dispersou os soberbos no pensamento dos seus corações.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 Derrubou os poderosos dos tronos, e elevou os humildes.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 Encheu de bens aos famintos, e despediu vazios os ricos.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 Auxiliou ao seu servo Israel, lembrando-se da [sua] misericórdia,
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 como falou aos nossos ancestrais, a Abraão, e à sua descendência, para sempre. (aiōn )
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
56 Maria esteve com ela por quase três meses; então voltou para sua casa.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 E completou-se à Isabel o tempo de dar à luz, e teve um filho.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 Os seus vizinhos e parentes ouviram que o Senhor havia feito a ela grande misericórdia, e alegraram-se com ela.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 E aconteceu que ao oitavo dia vieram circuncidar o menino, e o chamavam Zacarias, do nome do seu pai.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 E sua mãe respondeu: Não, porém será chamado João.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 E disseram-lhe: Ninguém há entre os teus parentes que se chame deste nome.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 E perguntaram por gestos ao seu pai como queria que lhe chamassem.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 Ele pediu uma tábua, e escreveu: O seu nome é João. E todos se surpeenderam.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 E logo a sua boca se abriu, e a sua língua se [soltou]; e voltou a falar, louvando a Deus.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 E veio temor sobre todos os seus vizinhos; e em toda a região montanhosa da Judeia todas essas coisas foram divulgadas.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 E todos os que ouviam, guardavam em seus corações, dizendo: Quem será este menino? Pois também a mão do Senhor estava com ele.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 E Zacarias, seu pai, foi cheio do Espírito Santo, e profetizou, dizendo:
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 Bendito [seja] o Senhor Deus de Israel, porque visitou e redimiu o seu povo.
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 E nos levantou uma poderosa salvação na casa de seu servo Davi,
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 como falou pela boca dos seus santos profetas, desde o princípio do mundo; (aiōn )
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
71 Que [nos] livraria dos nossos inimigos e da mão de todos os que nos odeiam,
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 para manifestar misericórdia aos nossos ancestrais, e se lembrar do seu santo pacto,
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 do juramento que fez a Abraão, nosso ancestral;
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 de nos conceder que, libertos da mão dos inimigos, o serviríamos sem temor,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 em santidade e justiça diante dele, todos os nossos dias.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 E tu, menino, serás chamado profeta do Altíssimo; porque irás adiante da face do Senhor, para preparar os seus caminhos,
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 para dar a seu povo conhecimento da salvação, na remissão de seus pecados;
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 por causa da profunda misericórdia do nosso Deus, pela qual o raiar da manhã nos visitará;
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 para iluminar os que estão sentados nas trevas e sombra de morte; a fim de guiar os nossos pés pelo caminho da paz.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 E o menino crescia e se fortalecia em espírito. E esteve nos desertos até o dia em que se mostrou a Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.