< Lamentações de Jeremias 3 >
1 Eu sou o homem que viu a aflição pela vara de seu furor.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Guiou-me e levou-me a trevas, e não à luz.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Com certeza se virou contra mim, revirou sua mão o dia todo.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Fez envelhecer minha carne e minha pele, quebrou meus ossos.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Edificou contra mim, e cercou [-me] de fel e de trabalho.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 Fez-me habitar em lugares escuros, como os que já morrera há muito tempo.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Cercou-me por todos lados, e não posso sair; tornou pesados os meus grilhões.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Até quando clamo e dou vozes, fechou [os ouvidos] à minha oração.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Cercou meus caminhos com pedras lavradas, retorceu as minhas veredas.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Foi para mim como um urso que espia, como um leão escondido.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Desviou meus caminhos, e fez-me em pedaços; deixou-me desolado.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Armou seu arco, e me pôs como alvo para a flecha.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Fez entrar em meus rins as flechas de sua aljava.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Servi de escárnio a todo o meu povo, de canção ridícula deles o dia todo.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Fartou-me de amarguras, embebedou-me de absinto.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Quebrou os meus dentes com cascalho, cobriu-me de cinzas.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 E afastou minha alma da paz, fez-me esquecer da boa vida.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 Então eu disse: Pereceram minha força e minha esperança no SENHOR.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Lembra-te da minha aflição e do meu sofrimento, do absinto e do fel.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Minha alma se lembra e se abate em mim.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Disto me recordarei na minha mente, por isso terei esperança:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 É pelas bondades do SENHOR que não somos consumidos, porque suas misericórdias não têm fim.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 Elas são novas a cada manhã; grande é a tua fidelidade.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 O SENHOR é minha porção, diz a minha alma; portanto nele esperarei.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Bom é o SENHOR para os que nele esperam, para a alma que o busca.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 É bom esperar e tranquilo aguardar a salvação do SENHOR.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 É bom ao homem levar o jugo em sua juventude.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Sente-se só, e fique quieto; pois ele o pôs sobre si.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Ponha sua boca no pó; talvez haja esperança.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Dê a face ao que o ferir; farte-se de insultos.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Pois o Senhor não rejeitará para sempre:
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Mesmo que cause aflição, ele também se compadecerá segundo a grandeza de suas misericórdias.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Pois não é sua vontade afligir nem entristecer os filhos dos homens.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Esmagar debaixo de seus pés a todos os prisioneiros da terra,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 Perverter o direito do homem diante da presença do Altíssimo,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 Prejudicar ao homem em sua causa: o Senhor não aprova ) [tais coisas].
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Quem é que pode fazer suceder [algo] que diz, se o Senhor não tiver mandado?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Por acaso da boca do Altíssimo não sai tanto a maldição como a bênção?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Por que o homem vivente se queixa da punição de seus próprios pecados?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Examinemos nossos caminhos, investiguemos, e nos voltemos ao SENHOR.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Levantemos nossos corações e as mãos a Deus nos céus,
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 [Dizendo: ] Nós transgredimos e fomos rebeldes; tu não perdoaste.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Cobriste-te de ira, e nos perseguiste; mataste sem teres compaixão.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Cobriste-te de nuvens, para que [nossa] oração não passasse.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Tu nos tornaste como escória e rejeito no meio dos povos.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Todos os nossos inimigos abriram sua boca contra nós.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Medo e cova vieram sobre nós, devastação e destruição.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Rios de águas correm de meus olhos, por causa da destruição da filha de meu povo.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Meus olhos destilam, e não cessam; não haverá descanso,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Até que o SENHOR preste atenção, e veja desde os céus.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Meus olhos afligem minha alma, por causa de todas as filhas de minha cidade.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Sem motivo meus inimigos me caçam como a um passarinho.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 Tentaram tirar minha vida na masmorra, e lançaram pedras sobre mim.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 As águas inundaram sobre minha cabeça; eu disse: É o meu fim.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Invoquei o teu nome, SENHOR, desde a cova profunda.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Ouviste minha voz: não escondas o teu ouvido ao meu suspiro, ao meu clamor.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Tu te achegaste no dia em que te invoquei; disseste: Não temas.
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Defendeste, Senhor, as causas de minha alma; redimiste minha vida.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Viste, SENHOR, a maldade que me fizeram; julga minha causa.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Viste toda a vingança deles, todos os seus pensamentos contra mim.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Ouvido os seus insultos, ó SENHOR, todos os seus pensamentos contra mim;
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 As coisas ditas pelos que se levantam contra mim, e seu planos contra mim o dia todo.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Olha para tudo quanto eles fazem; com canções zombam de mim.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Retribui-lhes, SENHOR, conforme a obra de suas mãos.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Dá-lhes angústia de coração, tua maldição a eles.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Persegue-os com ira, e destrua-os de debaixo dos céus do SENHOR.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.