< João 7 >
1 E depois disto andava Jesus na Galileia; e já não queria andar na Judeia, porque os judeus procuravam matá-lo.
Bayan wadannan abubuwa Yesu ya zagaya cikin Gallili, saboda baya so ya shiga cikin Yahudiya domin Yahudawa suna shirin su kashe shi.
2 E já estava perto a festa dos tabernáculos dos judeus.
To Idin Bukkoki na Yahudawa ya kusa.
3 Disseram-lhe pois seus irmãos: Parti daqui, e vai-te para a Judeia, para que também teus discípulos vejam as tuas obras que fazes.
Sai 'yan'uwansa suka ce da shi, “ka tashi ka tafi Yahudiya, domin almajiranka su ga ayyukan da kake yi su ma.
4 Pois ninguém que procura ser conhecido faz coisa alguma em oculto. Se fazes estas coisas, manifesta-te ao mundo.
Ba wanda ya ke yin wani abu a boye idan dai yana so kowa da kowa ya san shi. Da yake ka na yin wadannan abubuwa sai ka nuna kan ka a fili ga duniya.
5 Porque nem mesmo os seus irmãos criam nele.
Domin ko 'yan'uwansa ma basu bada gaskiya gare shi ba.
6 Então Jesus lhes disse: Meu tempo ainda não é chegado; mas vosso tempo sempre está pronto.
Yesu ya ce dasu, “lokaci na bai yi ba tukuna, amma ku koyaushe lokacin ku ne.
7 O mundo não pode vos odiar, mas a mim me odeia, porque dele testemunho que suas obras são más.
Duniya baza ta iya kin ku ba, amma ta ki ni saboda ina fadin cewa ayyukanta ba su da kyau.
8 Subi vós para esta festa; eu não subo ainda a esta festa, porque ainda meu tempo não é cumprido.
Ku ku je wurin idin, ni ba zan je wurin idin ba domin lokacina bai yi ba tukuna.
9 E havendo-lhes dito isto, ficou na Galileia.
Bayan da ya gaya masu wadannan abubuwa, ya tsaya a cikin Gallili.
10 Mas havendo seus irmãos já subido, então subiu ele também à festa, não abertamente, mas como em oculto.
Amma bayan da 'yan'uwansa su ka tafi wurin idin shi ma ya tafi, amma a asirce ba a fili ba.
11 Buscavam-no pois os judeus na festa, e diziam: Onde ele está?
Saboda Yahudawa suna neman sa a wurin idin, su na cewa “Ina yake?”
12 E havia grande murmuração dele nas multidões. Alguns diziam: Ele é Bom; e outros diziam: Não; ele, porém, engana a multidão.
Akwai maganganu dayawa a kansa cikin taron. Wadansu suna cewa, “shi mutumin kirki ne.” Wadansu kuma suna cewa,”A'a yana karkatar da hankalin jama'a.”
13 Todavia ninguém falava dele abertamente, com medo dos judeus.
Amma duk da haka ba wanda ya yi magana a fili a kansa saboda suna jin tsoron Yahudawa.
14 Porém no meio da festa subiu Jesus ao Templo, e ensinava.
Sa'anda aka kai rabin idin, sai Yesu ya shiga cikin haikali ya fara koyarwa.
15 E maravilhavam-se os Judeus, dizendo: Como este sabe as Escrituras, não as havendo aprendido?
Yahudawa suna mamaki suna cewa,”Yaya aka yi wannan mutum ya sami ilimi dayawa haka? Shi kuwa bai je makaranta ba.”
16 Respondeu-lhes Jesus, e disse: Minha doutrina não é minha, mas sim daquele que me enviou.
Yesu ya ba su amsa ya ce,”Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce.”
17 Se alguém quiser fazer sua vontade, da doutrina conhecerá, se é de Deus, ou [se] eu falo de mim mesmo.
Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina.
18 Quem fala de si mesmo busca sua própria honra; mas quem busca a honra daquele que o enviou, esse é verdadeiro, e não há nele injustiça.
Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.
19 Não vos deu Moisés a Lei? Mas ninguém de vós cumpre a Lei. Por que procurais me matar?
Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni?
20 Respondeu a multidão, e disse: Tens demônio; quem procura te matar?
Taron suka ba shi amsa, “Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?”
21 Respondeu Jesus, e disse-lhes: Uma obra fiz, e todos vos maravilhais.
Yesu ya amsa ya ce masu, “Nayi aiki daya, dukan ku kuna mamaki da shi.
22 Por isso Moisés vos deu a circuncisão (não porque seja de Moisés, mas dois pais) e no sábado circuncidais ao homem.
Musa ya baku kaciya, (ba kuwa daga Musa take ba, amma daga kakannin kakanni ta ke), kuma a ranar Asabar kukan yi wa mutum kaciya.
23 Se o homem recebe a circuncisão no sábado, para que a Lei de Moisés não seja quebrada, irritai-vos comigo, porque no sábado curei por completo um homem?
Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar?
24 Não julgueis segundo a aparência, mas julgai juízo justo.
Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci.”
25 Diziam, pois, alguns dos de Jerusalém: Não é este ao que procuram matar?
Wadansun su daga Urushalima suka ce, “wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?”
26 E eis que ele fala livremente, e nada lhe dizem; por acaso é verdade que os chefes sabem que este realmente é o Cristo?
Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba?
27 Mas este bem sabemos de onde é: Porém quando vier o Cristo, ninguém saberá de onde é.
da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito.”
28 Exclamava pois Jesus no Templo, ensinando, e dizendo: E a mim me conheceis, e sabeis de onde sou; e eu não vim de mim mesmo; mas aquele que me enviou é verdadeiro, ao qual vós não conheceis.
Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, “Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba.
29 Porém eu o conheço, porque dele sou, e ele me enviou.
Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni.”
30 Procuravam pois prendê-lo, mas ninguém pôs a mão nele, porque sua hora ainda não era vinda.
Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna.
31 E muitos da multidão creram nele, e diziam: Quando o Cristo vier, fará ainda mais sinais do que os que este tem feito?
Duk da haka wadansu dayawa a cikin taron suka bada gaskiya gare shi suka ce,”Sa'anda Kristi ya zo, zai yi alamu fiye da wadanda wannan mutum ya yi?”
32 Ouviram os fariseus que a multidão murmurava estas coisas sobre ele; e os fariseus e os chefes dos Sacerdotes mandaram oficiais para prendê-lo.
Farisawa suka ji tattarmukan suna yin rada a kan wadannan abubuwa game da Yesu, Sai manyan malamai da Farisawa su ka aika jami'ai su kama shi.
33 Disse-lhes pois Jesus: Ainda um pouco de tempo estou convosco, e [então] me irei para aquele que me enviou.
Sa'annan Yesu yace ma su,” jimawa kadan ina tare ku, sa'annan in tafi wurin wanda ya aiko ni.
34 Vós me buscareis, mas não [me] achareis; e onde eu estou vós não podeis vir.
Za ku neme ni ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba.”
35 Disseram, pois, os judeus uns aos outros: Para onde este se irá, que não o acharemos? Por acaso ele irá aos dispersos entre os gregos, e a ensinar aos gregos?
Yahudawa fa su ka cewa junan su, “Ina wannan mutum zai je inda ba za mu iya samun sa ba? Ko za ya tafi wurin Helinawa na warwatsuwa ya koyawa Helinawa?
36 Que palavra é esta que disse: Vós me buscareis, mas não [me] achareis; e onde eu estou vós não podeis vir?
Wace kalma ya ke fadi haka, 'za ku neme ni amma ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba'?”
37 E no último e grande dia da festa se pôs Jesus em pé, e exclamou, dizendo: Se alguém tem sede, venha a mim, e beba.
To a rana ta karshe, babbar rana ta idin, Yesu ya mike ya yi magana da karfi cewa, “Idan kowa yana jin kishi, ya zo wuri na ya sha.
38 Quem crê em mim, como diz a Escritura, rios de água viva correrão do interior de seu corpo.
Shi wanda ya bada gaskiya gare ni kamar yadda nassi ya fadi, daga cikin sa rafukan ruwa na rai za su bulbulo.”
39 (E ele disse isto do Espírito que receberiam aqueles que nele cressem; pois o Espírito Santo ainda não era [vindo], porque Jesus ainda não havia sido glorificado).
Amma ya fadi haka a kan Ruhu, wanda wadanda suka bada gaskiya gare shi za su karba; ba a ba da Ruhun ba tukuna, saboda ba a rigaya an daukaka Yesu ba.
40 Então muitos da multidão, ouvindo esta palavra, diziam: Verdadeiramente este é o Profeta.
Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, “Wannan lallai annabi ne.”
41 Outros diziam: Este é o Cristo; e outros diziam: Por acaso vem o Cristo da Galileia?
Wadansu suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma wadansu suka ce, “Almasihu zai fito daga Gallili ne?
42 Não diz a Escritura que o Cristo virá da semente de Davi, e da aldeia de Belém, de onde era Davi?
Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?”
43 Por isso havia divisão de opiniões na multidão por causa dele.
Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi.
44 E alguns deles queriam prendê-lo, mas ninguém pôs a mão nele.
Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.
45 Vieram pois os oficiais dos sacerdotes e fariseus; e eles lhes disseram: Por que não o trouxestes?
Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce,” me yasa ba ku kawo shi ba?”
46 Os oficiais responderam: Ninguém jamais falou assim como este homem.
Jami'an su ka amsa, “Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka.”
47 Responderam-lhes, pois, os fariseus: Estais vós também enganados?
Farisawa suka amsa masu, “kuma an karkatar da ku?
48 Por acaso algum dos chefes ou dos fariseus creu nele?
Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa?
49 Mas esta multidão, que não sabe a Lei, maldita é.
Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne.”
50 Disse-lhes Nicodemos, o que viera a ele de noite, que era um deles:
Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa),
51 Por acaso nossa Lei julga ao homem sem primeiro o ouvir, e entender o que faz?
“Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?”
52 Responderam eles, e disseram: És tu também da Galileia? Pesquisa, e vê que nenhum profeta se levantou da Galileia.
Suka amsa masa suka ce,”kai ma daga Galili ka fito? Ka yi bincike ka gani ba annanbin da zai fito daga Galili.”
53 «E cada um foi para sua casa.
Daga nan sai kowa ya tafi gidansa.