< Jó 7 >
1 Por acaso o ser humano não tem um trabalho duro sobre a terra, e não são seus dias como os dias de um assalariado?
“Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
2 Como o servo suspira pela sombra, e como o assalariado espera por seu pagamento,
Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
3 Assim também me deram por herança meses inúteis, e me prepararam noites de sofrimento.
Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
4 Quando eu me deito, pergunto: Quando me levantarei? Mas a noite se prolonga, e me canso de me virar [na cama] até o amanhecer.
Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
5 Minha carne está coberta de vermes e de crostas de pó; meu pele está rachada e horrível.
Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
6 Meus dias são mais rápidos que a lançadeira do tecelão, e perecem sem esperança.
“Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
7 Lembra-te que minha vida é um sopro; meus olhos não voltarão a ver o bem.
Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
8 Os olhos dos que me veem não me verão mais; teus olhos estarão sobre mim, porém deixarei de existir.
Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
9 A nuvem se esvaece, e passa; assim também quem desce ao Xeol nunca voltará a subir. (Sheol )
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
10 Nunca mais voltará à sua casa, nem seu lugar o conhecerá.
Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
11 Por isso eu não calarei minha boca; falarei na angústia do meu espírito, e me queixarei na amargura de minha alma.
“Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
12 Por acaso sou eu o mar, ou um monstro marinho, para que me ponhas guarda?
Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
13 Quando eu digo: Minha cama me consolará; meu leito aliviará minhas queixa,
Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
14 Então tu me espantas com sonhos, e me assombras com visões.
duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
15 Por isso minha alma preferia a asfixia [e] a morte, mais que meus ossos.
Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
16 Odeio [a minha vida]; não viverei para sempre; deixa-me, pois que meus dias são inúteis.
Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
17 O que é o ser humano, para que tanto o estimes, e ponhas sobre ele teu coração,
“Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
18 E o visites a cada manhã, e a cada momento o proves?
har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
19 Até quando não me deixarás, nem me liberarás até que eu engula minha saliva?
Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
20 Se pequei, o eu que te fiz, ó Guarda dos homens? Por que me fizeste de alvo de dardos, para que eu seja pesado para mim mesmo?
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
21 E por que não perdoas minha transgressão, e tiras minha maldade? Porque agora dormirei no pó, e me buscarás de manhã, porém não mais existirei.
Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”