< Jó 37 >
1 Disto também o meu coração treme, e salta de seu lugar.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Ouvi atentamente o estrondo de sua voz, e o som que sai de sua boca,
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Ao qual envia por debaixo de todos os céus; e sua luz até os confins da terra.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Depois disso brama com estrondo; troveja com sua majestosa voz; e ele não retém [seus relâmpagos] quando sua voz é ouvida.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Deus troveja maravilhosamente com sua voz; ele faz coisas tão grandes que nós não compreendemos.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Pois ele diz à neve: Cai sobre à terra; Como também à chuva: Sê chuva forte.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Ele sela as mãos de todo ser humano, para que todas as pessoas conheçam sua obra.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 E os animais selvagens entram nos esconderijos, e ficam em suas tocas.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Da recâmara vem o redemoinho, e dos [ventos] que espalham [vem] o frio.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Pelo sopro de Deus se dá o gelo, e as largas águas se congelam.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Ele também carrega de umidade as espessas nuvens, [e] por entre as nuvens ele espalha seu relâmpago.
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 Então elas se movem ao redor segundo sua condução, para que façam quanto ele lhes manda sobre a superfície do mundo, na terra;
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 Seja que ou por vara de castigo, ou para sua terra, ou por bondade as faça vir.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Escuta isto, Jó; fica parado, e considera as maravilhas de Deus.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Por acaso sabes tu quando Deus dá ordem a elas, e faz brilhar o relâmpago de sua nuvem?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Conheces tu os equilíbrios das nuvens, as maravilhas daquele que é perfeito no conhecimento?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Tu, cujas vestes se aquecem quando a terra se aquieta por causa do [vento] sul,
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 acaso podes estender com ele os céus, que estão firmes como um espelho fundido?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Ensina-nos o que devemos dizer a ele; [pois discurso] nenhum podemos propor, por causa das [nossas] trevas.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Seria contado a ele o que eu haveria de falar? Por acaso alguém falaria para ser devorado?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 E agora não se pode olhar para o sol, quando brilha nos céus, quando o vento passa e os limpa.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Do norte vem o esplendor dourado; em Deus há majestade temível.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 Não podemos alcançar ao Todo-Poderoso; ele é grande em poder; porém ele a ninguém oprime [em] juízo e grandeza de justiça.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Por isso as pessoas o temem; ele não dá atenção aos que [se acham] sábios de coração.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”