< Jó 32 >
1 Então aqueles três homens cessaram de responder a Jó, porque ele era justo em seus olhos.
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 Porém se acendeu a ira de Eliú, filho de Baraquel, buzita, da família de Rão; contra Jó se acendeu sua ira, porque justificava mais a si mesmo que a Deus.
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 Também sua ira se acendeu contra seus três amigos, porque não achavam o que responder, ainda que tinham condenado a Jó.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 E Eliú tinha esperado a Jó naquela discussão, porque tinham mais idade que ele.
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 Porém quando Eliú viu que não havia resposta na boca daqueles três homens, sua ira se acendeu.
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 Por isso Eliú, filho de Baraquel, buzita, respondeu, dizendo: Eu sou jovem e vós sois idosos; por isso fiquei receoso e tive medo de vos declarar minha opinião.
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 Eu dizia: Os dias falem, e a multidão de anos ensine sabedoria.
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 Certamente há espírito no ser humano, e a inspiração do Todo-Poderoso os faz entendedores.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 Não são [somente] os grandes que são sábios, nem [somente] os velhos entendem o juízo.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 Por isso eu digo: escutai-me; também eu declararei minha opinião.
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 Eis que eu aguardei vossas palavras, [e] dei ouvidos a vossas considerações, enquanto vós buscáveis argumentos.
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 Eu prestei atenção a vós, porém eis que ninguém há de vós que possa convencer a Jó, [nem] que responda a suas palavras.
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 Portanto não digais: Encontramos a sabedoria; que Deus o derrote, [e] não o homem.
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 Jó não dirigiu suas palavras a mim, nem eu lhe responderei com vossos dizeres.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 Estão pasmos, não respondem mais; faltam-lhes palavras.
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 Esperei, pois, porém [agora] não falam; porque já pararam, [e] não respondem mais.
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 Também eu responderei minha parte; também eu declararei minha opinião.
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 Porque estou cheio de palavras, e o espírito em meu ventre me obriga.
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 Eis que meu ventre é como o vinho que não tem abertura; e que está a ponto de arrebentar como odres novos.
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 Falarei, para que eu me alivie; abrirei meus lábios, e responderei.
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 Não farei eu acepção de pessoas, nem usarei de títulos lisonjeiros para com o homem.
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 Pois não sei lisonjear; [caso contrário], meu Criador logo me removeria.
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.