< 31 >

1 Eu fiz um pacto com meus olhos; como, pois, eu olharia com cobiça para a virgem?
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 Pois qual é a porção [dada] por Deus acima, e a herança [dada] pelo Todo-Poderoso das alturas?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Por acaso a calamidade não é para o perverso, e o desastre para os que praticam injustiça?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Por acaso ele não vê meus caminhos, e conta todos os meus passos?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Se eu andei com falsidade, e se meu pé se apressou para o engano,
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 Pese-me ele em balanças justas, e Deus saberá minha integridade.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 Se meus passos se desviaram do caminho, e meu coração seguiu meus olhos, e se algo se apegou às minhas mãos,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 Que eu semeie, e outro coma; e meus produtos sejam arrancados.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Se foi meu coração se deixou seduzir por [alguma] mulher, ou se estive espreitei à porta de meu próximo,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 Que minha mulher moa para outro, e outros se encurvem sobre ela.
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Pois tal seria um crime vergonhoso, e delito [a ser sentenciado por] juízes.
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 Pois seria um fogo que consumiria até à perdição, e destruiria toda a minha renda.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Se desprezei o direito de meu servo ou de minha serva quando eles reclamaram comigo,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 Que faria eu quando Deus se levantasse? E quando ele investigasse [a causa], o que eu lhe responderia?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Aquele que me fez no ventre [materno também] não fez a ele? E não nos preparou de um mesmo [modo] na madre?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 Se eu neguei aos pobres o que eles desejavam, ou fiz desfalecer os olhos da viúva;
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 E se comi meu alimento sozinho, e o órfão não comeu dele
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 (Porque desde a minha juventude cresceu comigo como [se eu fosse seu pai], e desde o ventre de minha mãe guiei [a viúva] );
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 Se eu vi alguém morrer por falta de roupa, e o necessitado sem algo que o cobrisse,
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 Se sua cintura não me bendisse, quando ele se esquentava com as peles de meus cordeiros;
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 Se levantei minha mão contra o órfão, quando vi que seria favorecido na corte judicial,
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 Que minha escápula caia do meu ombro, e meu braço se quebre de sua articulação.
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Porque o castigo de Deus era um assombro para mim, e eu não teria poder contra sua majestade.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Se eu pus no ouro minha esperança, ou disse ao ouro fino: Tu és minha confiança;
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 Se eu me alegrei de que minha riqueza era muita, e de que minha mão havia obtido muito;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 Se olhei para o sol quando brilhava, e à lua quando estava bela,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 E meu coração se deixou enganar em segredo, e minha boca beijou minha mão,
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 Isto também seria um delito [a ser sentenciado por] juiz; porque teria negado ao Deus de cima.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 Se eu me alegrei da desgraça daquele que me odiava, e me agradei quando o mal o encontrou,
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 Sendo que nem deixei minha boca pecar, desejando sua morte com maldição,
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 Se a gente da minha casa nunca tivesse dito: Quem não se satisfez da carne dada por ele?
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 O estrangeiro não passava a noite na rua; eu abria minhas portas ao viajante.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 Se encobri minhas transgressões como as pessoas [fazem], escondendo meu delito em meu seio;
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 Porque eu tinha medo da grande multidão, e o desprezo das famílias me atemorizou; então me calei, e não saí da porta:
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 Quem me dera se alguém me ouvisse! Eis que minha vontade é que o Todo-Poderoso me responda, e meu adversário escrevesse um relato da acusação.
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Certamente eu o carregaria sobre meu ombro, e o poria em mim como uma coroa.
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Eu lhe diria o número de meus passos, e como um príncipe eu me chegaria a ele.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Se minha terra clamar contra mim, e seus sulcos juntamente chorarem;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 Se comi seus frutos sem [pagar] dinheiro, ou fiz expirar a alma de seus donos;
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 Em lugar de trigo que [me] produza cardos, e ervas daninhas no lugar da cevada. [Aqui] terminam as palavras de Jó.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< 31 >