< Jó 26 >
1 Porém Jó respondeu, dizendo:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Como tende ajudado ao que não tem força, [e] sustentado ao braço sem vigor!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 Como tende aconselhado ao que não tem conhecimento, e [lhe] explicaste detalhadamente a verdadeira causa!
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 A quem tens dito [tais] palavras? E de quem é o espírito que sai de ti?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 Os mortos tremem debaixo das águas com os seus moradores.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 O Xeol está nu perante Deus, e não há cobertura para a perdição. (Sheol )
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
7 Ele estende o norte sobre o vazio, suspende a terra sobre o nada.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 Ele amarra as águas em suas nuvens, todavia a nuvem não se rasga debaixo dela.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 Ele encobre a face de seu trono, e sobre ele estende sua nuvem.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 Ele determinou limite à superfície das águas, até a fronteira entre a luz e as trevas.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 As colunas do céu tremem, e se espantam por sua repreensão.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 Ele agita o mar com seu poder, e com seu entendimento fere abate a Raabe.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 Por seu Espírito adornou os céus; sua mão perfurou a serpente veloz.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Eis que estas são [somente] as bordas de seus caminhos; e quão pouco é o que temos ouvido dele! Quem, pois, entenderia o trovão de seu poder?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”