< Jó 19 >
1 Porém Jó respondeu dizendo:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Até quando atormentareis minha alma, e me quebrantareis com palavras?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Já dez vezes me humilhastes; não tendes vergonha em me maltratar.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 Mesmo se eu tiver errado, meu erro cabe apenas a mim.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 Visto que vos exaltais contra mim, e contra mim usais minha desgraça,
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Sabei, pois, que foi Deus que me transtornou, e [com] sua rede me cercou.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Eis que eu clamo: Violência! Porém não sou respondido; grito, porém não há justiça.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 Ele entrincheirou meu caminho, de modo que não consigo passar; e pôs trevas sobre minhas veredas.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 Ele me despojou de minha honra, e tirou a coroa de minha cabeça.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 Ele me derrubou por todos os lados, e pereço; e arrancou minha esperança como a uma árvore.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 E fez inflamar contra mim sua ira, e me considerou para consigo como a [um de] seus inimigos.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 Juntas vieram suas tropas; prepararam contra mim seu caminho, e se acamparam ao redor de minha tenda.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 Ele afastou meus irmãos para longe de mim; e os que me conheciam agora me estranham.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 Meus parentes [me] deixaram, e meus conhecidos se esqueceram de mim.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 Os moradores de minha casa e minhas servas me tiveram por estranho; estrangeiro me tornei em seus olhos.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 Chamei a meu servo, e ele não respondeu; de minha própria boca eu lhe suplicava.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 Meu hálito é estranho à minha mulher, e sou repugnante aos filhos de minha mãe.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Até os meninos me desprezam; quando eu me levanto, falam contra mim.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 Todos os meus amigos próximos me abominam; e [até] aqueles que eu amava se viraram contra mim.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 Meus ossos se grudaram à minha pele e à minha carne; e escapei [só] com a pele de meus dentes.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Compadecei-vos de mim, meus amigos, compadecei-vos de mim; pois a mão de Deus me tocou.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Por que vós me perseguis como Deus, e não vos fartais de minhas carne?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Ah se minhas palavras fossem escritas! Ah se fossem escritas em um livro!
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 Que com ponta de ferro e com chumbo fossem esculpidas em pedra para sempre!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 Pois eu sei que meu Redentor vive, e ao fim se levantará sobre a terra;
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 E mesmo depois de consumida minha pele, então em minha carne verei a Deus;
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Ao qual eu verei para mim, e meus olhos [o] verão, e não outro. [Isto é o que] minhas entranhas anseiam dentro de mim.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 Se disserdes: Como o perseguiremos? Pois a raiz do problema se acha em mim,
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Temei vós mesmos a espada; pois furor [há nos] castigos pela espada; para que [assim] saibais que [haverá] julgamento.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”