< 12 >

1 Porém Jó respondeu, dizendo:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Verdadeiramente vós sois o povo; e convosco morrerá a sabedoria.
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 Também eu tenho entendimento como vós; e não sou inferior a vós; e quem há que não saiba coisas como essas?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 Eu sou o motivo de riso de meus amigos, eu que invocava a Deus, e ele me respondia; o justo e íntegro serve de riso.
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 Na opinião de quem está descansado, a desgraça é desprezada, [como se] estivesse preparada aos que cujos pés escorregam.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 As tendas dos ladrões têm descanso, e os que irritam a Deus estão seguros; os que trazem [seu] deus em suas mãos.
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 Verdadeiramente pergunta agora aos animais, que eles te ensinarão; e às aves dos céus, que elas te explicarão;
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 Ou fala com a terra, que ela te ensinará; até os peixes do mar te contarão.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Quem entre todas estas coisas não entende que a mão do SENHOR faz isto?
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 Em sua mão está a alma de tudo quanto vive, e o espírito de toda carne humana.
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Por acaso o ouvido não distingue as palavras, e o paladar prova as comidas?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 Nos velhos está o conhecimento, e na longa idade o entendimento.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 Com [Deus] está a sabedoria e a força; o conselho e o entendimento lhe pertencem.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Eis que o que ele derruba não pode ser reconstruído; e ninguém pode libertar o homem a quem ele aprisiona.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Eis que, [quando] ele detém as águas, elas se secam; [quando] ele as deixa sair, elas transtornam a terra.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 Com ele está a força e a sabedoria; Seu é o que erra, e o que faz errar.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 Ele leva os conselheiros despojados, e faz os juízes enlouquecerem.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 Ele solta a atadura dos reis, e ata um cinto a seus lombos.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 Ele leva os sacerdotes despojados, e transtorna os poderosos.
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 Ele tira a fala daqueles a quem os outros confiam, e tira o juízo dos anciãos.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 Ele derrama menosprezo sobre os príncipes, e afrouxa o cinto dos fortes.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 Ele revela as profundezas das trevas, e traz a sombra de morte à luz.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 Ele multiplica as nações, e ele as destrói; ele dispersa as nações, e as reúne.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 Ele tira o entendimento dos líderes do povo da terra, e os faz vaguear pelos desertos, sem caminho.
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 Nas trevas andam apalpando, sem terem luz; e os faz cambalear como a bêbados.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.

< 12 >