< Jó 11 >
1 Então Zofar, o naamita, respondeu, dizendo:
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Por acaso a multidão de palavras não seria respondida? E o homem falador teria razão?
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 Por acaso tuas palavras tolas faria as pessoas se calarem? E zombarias tu, e ninguém te envergonharia?
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 Pois disseste: Minha doutrina é pura, e eu sou limpo diante de teus olhos.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 Mas na verdade, queria eu que Deus falasse, e abrisse seus lábios contra ti,
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 E te fizesse saber os segredos da sabedoria, porque o verdadeiro conhecimento tem dois lados; por isso sabe tu que Deus tem te castigado menos que [mereces] por tua perversidade.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Podes tu compreender os mistérios de Deus? Chegarás tu à perfeição do Todo-Poderoso?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 [Sua sabedoria] é mais alta que os céus; que tu poderás fazer? E mais profunda que o Xeol; que tu poderás conhecer? (Sheol )
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
9 Sua medida é mais comprida que a terra, e mais larga que o mar.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 Se ele passar, e prender, ou se ajuntar [para o julgamento], quem poderá o impedir?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 Pois ele conhece as pessoas vãs, e vê a maldade; por acaso ele não a consideraria?
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 O homem tolo se tornará entendido quando do asno selvagem nascer um humano.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 Se tu preparares o teu coração, e estenderes a ele tuas mãos;
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 Se alguma maldade houver em tua mão, lança-a de ti, e não deixes a injustiça habitar em tuas tendas;
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 Então levantarás teu rosto sem mácula; estarás firme, e não temerás;
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 E esquecerás teu sofrimento, [ou] lembrarás dele como de águas que já passaram;
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 E [tua] vida será mais clara que o meio-dia; ainda que haja trevas, tu serás como o amanhecer.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 E serás confiante, porque haverá esperança; olharás em redor, [e] repousarás seguro.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 E te deitarás, e ninguém te causará medo; e muitos suplicarão a ti.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 Porém os olhos dos maus se enfraquecerão, e o refúgio deles perecerá; a esperança deles será a morte.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”