< Tiago 4 >

1 De onde [vêm] as guerras e brigas entre vós? Acaso não [vêm] disto, das vossas cobiças que guerreiam nos membros do vosso corpo?
Me ke kawo gaba da rashin jituwa a tsakanin ku? Ba yana tasowa ne daga muguwar sha'awa da ke yaki a cikin ku ba?
2 Cobiçais, e nada tendes; matais e sois invejosos, mas não conseguis obter; combateis e guerreais, mas nada tendes, porque não pedis.
Kuna sha'awa, kuma ba ku da shi. Kuna kisa da kyashi, kuma ba za ku iya samu ba. Kuna danbe da fada. Har wa yau baku samu ba domin baku tambaya ba.
3 Pedis, e não recebeis, porque pedis mal, para gastardes nos vossos prazeres.
Kun roka kuma ba a baku ba saboda kuna roko ta hanya mara kyau, kuna so ku yi amfani da shi domin miyagun sha'awoyin ku.
4 Adúlteros e adúlteras, não sabeis que a amizade do mundo é inimizade contra Deus? Portanto, quem quiser ser amigo do mundo constitui-se inimigo de Deus.
Ku mazinata! Baku sani ba, abokantaka da duniya, tawaye ne ga Allah? Don haka duk wanda ya shiga abokantaka da duniya ya zama magabcin Allah.
5 Ou pensais ser em vão que a Escritura diz: “O Espírito que ele fez habitar em nós ansia com ciúmes?”
Ko kuna zaton nassi ya fadi haka a banza ne, “Ruhun nan da ke a cikinmu yana da kishi matuka?”
6 Porém ele concede uma graça maior. Por isso diz: Deus resiste aos soberbos, mas concede graça aos humildes.
Amma Allah ya bayar da karin alheri, shi ya sa nassi ya ce, “Allah yana gaba da mai girman kai, Amma yana ba da alheri ga mai tawaliu.”
7 Sujeitai-vos, pois, a Deus; resisti ao diabo, e ele fugirá de vós.
Saboda haka ku mika kan ku ga Allah. Ku yi tsayayya da shaidan, zai kuma guje maku.
8 Aproximai-vos de Deus, e ele se aproximará de vós. Limpai as [vossas] mãos, pecadores, e vós de dupla mentalidade, purificai os [vossos] corações.
Ku matso kusa da Allah, shi kuma za ya matsa kusa da ku. Wanke hannayen ku, ku masu zunubi, ku tsabtace zukatan ku, ku masu zuciya biyu.
9 Reconhecei vossas misérias, lamentai e chorai. Torne-se o vosso riso em pranto, e a [vossa] alegria em tristeza.
Ku yi bakin ciki, makoki, da kuka! Ku mayar da dariyar ku ta koma bakin ciki, farin cikinku kuma zuwa ga bakin ciki.
10 Humilhai-vos diante do Senhor, e ele vos exaltará.
Ku kaskantar da kanku a gaban Ubangiji, shi kuma za ya daukaka ku.
11 Irmãos, não faleis mal uns dos outros. Quem fala mal de um irmão, ou julga o seu irmão, fala mal da lei, e julga a lei. E se julgas a lei, não és um cumpridor da lei, mas, sim, juiz.
Kada ku rika zargin juna, 'yan'uwa. Wanda ya ke zargin dan'uwa ko shari'anta dan'uwansa, yana zargin shari'a kuma yana hukunta shari'a. Idan ka hukunta shari'a, ya nuna ba ka biyayya da shari'ar, amma mai hukunci.
12 Um [só] é o Legislador e Juiz, que pode salvar e destruir. Quem és tu, que julgas o próximo?
Mai ba da shari'a da yin hukunci daya ne. Shine mai iya ceto kuma ya hallakar. Kai wanene, da ke hukunta makwafcin ka?
13 Atenção! Vós que dizeis: “Hoje ou amanhã iremos a uma tal cidade, e lá passaremos um ano negociando e lucrando”;
Saurara, ku da kuke cewa, “Yau ko gobe za mu tafi wancan birnin mu yi shekara guda a wurin, muna kasuwanci, mu kuma yi riba.”
14 mas não sabeis o amanhã. Pois o que [é] a vossa vida? Sois um vapor, que por pouco tempo aparece, e logo se desvanece.
Wa ya san abin da zai faru gobe, kuma yaya rayuwan ka zai kasance? Kai kamar hazo ne mai bayyana bayan dan lokaci kadan ya bace.
15 Em vez disso, devíeis dizer: Se o Senhor quiser, e vivermos, faremos isso ou aquilo.
Maimakon haka, sai ka ce, “Idan Ubangiji ya nufa, za mu rayu kuma mu yi wannan ko wancan.”
16 Mas agora vos orgulhais nas vossas presunções; todo orgulho como esse é maligno.
Amma yanzu kana fahariya da shirye shiryen ka na takama. Irin wannan fahariya, mugunta ce.
17 Portanto, quem sabe fazer o bem, e não [o] faz, comete pecado.
Saboda haka ga wanda ya san abin da ya kamata ya aikata amma bai yi ba, ya zama zunubi a gare shi.

< Tiago 4 >