< Eclesiastes 7 >

1 Melhor é uma boa reputação do que o bom óleo perfumado; e o dia da morte [é melhor] que o dia de seu nascimento
Suna mai kyau ya fi turare mai ƙanshi, kuma ranar mutuwa ta fi ranar haihuwa.
2 Melhor é ir à casa do luto do que a casa do banquete, [porque] isto é o fim de todos os homens; e os vivos tomam isto em seus corações.
Gara a tafi gidan makoki da a je gidan biki, gama mutuwa ce ƙaddarar kowane mutum; ya kamata masu rai su lura da haka.
3 Melhor é o sofrimento do que o riso, porque com a tristeza do rosto o coração se aperfeiçoa.
Baƙin ciki ya fi dariya, gama baƙin ciki yakan kawo gyara.
4 O coração dos sábios está na casa do luto, mas o coração dos tolos [está] na casa da alegria.
Zuciyar masu hikima tana a gidan makoki, amma zuciya wawaye tana a gidan shagali.
5 Melhor é ouvir a repreensão do sábio do que alguém ouvir a canção dos tolos;
Gara ka saurari tsawatawar mai hikima da ka saurari waƙar wawaye.
6 Pois o riso dos tolos é como o ruído de espinhos debaixo de uma panela; também isto é futilidade.
Kamar ƙarar ƙayar da take karce gindin tukunya, haka dariyar wawaye take. Wannan ma ba shi da amfani.
7 Verdadeiramente a opressão faz até o sábio enlouquecer, e o suborno corrompe o coração.
Zalunci yakan mai da mutum mai hikima wawa, cin hanci kuma yakan lalace hali.
8 Melhor é o fim das coisas do que o princípio delas; melhor é o paciente de espírito do que o arrogante de espírito.
Ƙarshen abu ya fi farkonsa, haƙuri kuma ya fi girman kai.
9 Não te apresses em teu espírito para te irares, porque a ira repousa no colo dos tolos.
Kada ranka yă yi saurin tashi, gama fushi yana zama a cinyar wawaye.
10 Nunca digas: Por que os dias passados foram melhores que os atuais? Pois nunca com sabedoria perguntarias isso.
Kada ka ce, “Me ya sa kwanakin dā sun fi waɗannan?” Gama ba daidai ba ne a yi irin waɗannan tambayoyi.
11 A sabedoria é tão boa quanto uma herança; ela é um proveito para os que veem a luz do sol;
Hikima, kamar gādo, abu mai kyau ne tana kuma da amfani ga waɗanda suka ga rana.
12 porque a sabedoria serve de proteção, assim como o dinheiro serve de proteção; mas a vantagem do conhecimento é que a sabedoria dá vida ao seu dono.
Hikima mafaka ce takan kāre mutum kamar yadda kuɗi suke yi. Kiyayewar da hikima takan yi wa mai ita ita ce amfanin ilimi.
13 Observa a obra de Deus, pois quem poderá endireitar o que ele entortou?
Ku lura da abin da Allah ya yi. Wa zai iya miƙe abin da ya tanƙware?
14 No dia da prosperidade, alegra-te; mas no dia da adversidade, considera; pois Deus faz um em contraposição ao outro, para que o homem não consiga descobrir o que haverá depois dele.
Sa’ad da al’amura suke tafiya daidai, ka yi farin ciki, amma sa’ad da suka lalace, ka tuna, Allah ne ya yi wancan shi ne kuma ya yi wannan. Saboda haka, mutum ba zai san wani abu game da nan gabansa ba.
15 Tudo [isto] vi nos meus dias de futilidade: há justo que perece em sua justiça, e há perverso que prolonga [sua vida] em sua maldade.
A cikin rayuwan nan ta rashin amfani nawa, na lura da waɗannan abubuwa biyu, mai adalci yana hallakawa cikin adalcinsa, mai mugunta kuma yana tsawon rai cikin muguntarsa.
16 Não sejas justo demais, nem sejas sábio demais; para que destruirias a ti mesmo?
Kada ka cika yin adalci, fiye da kima, kada kuma ka cika yin hikima, don me za ka hallaka kanka!
17 Não sejas perverso demais, nem sejas tolo; para que morrerias antes de teu tempo?
Kada ka cika yin mugunta, kada kuma ka cika yin wauta, don me za ka mutu kafin lokacinka?
18 É bom que retenhas isto, e também não retires tua mão disto, pois quem teme a Deus escapa de tudo isto.
Yana da kyau ka kama ɗaya ba tare da ka saki wancan ba. Mai tsoron Allah zai guji wuce gona da iri.
19 A sabedoria fortalece ao sábio, mais do que dez homens de autoridade que estejam na cidade.
Hikima takan sa mutum guda mai hikima yă yi ƙarfi fiye da masu mulki goma a cikin birni.
20 Verdadeiramente não há homem justo sobre a terra, que faça o bem, e nunca peque.
Babu mai adalci a duniya wanda yake yin abin da yake daidai da bai taɓa yin zunubi ba.
21 Além disso, não dês atenção a todas as palavras que forem ditas, para que não venhas a ouvir que teu servo te amaldiçoa;
Kada ka mai da hankali ga dukan abin da mutane suke faɗi, in ba haka ba wata rana za ka ji bayinka suna zaginka.
22 Pois teu coração sabe que também tu já amaldiçoaste a outros.
Gama kai kanka ka sani cewa sau da yawa ka zagi waɗansu.
23 Tudo isto investiguei com sabedoria. Eu disse: Terei para mim mais sabedoria; porém ela ficava [ainda] mais longe de mim.
Dukan waɗannan na gwada su ta wurin hikima na kuma ce, “Na ƙudurta in zama mai hikima,” amma abin ya fi ƙarfina.
24 Quem pode encontrar o que está distante e tão profundo?
Ko da me hikima take, Abin ya yi mana zurfi ƙwarai, yana da wuyar ganewa, wa zai iya gane shi?
25 Decidi em meu coração conhecer, investigar e buscar a sabedoria e a razão; e saber o mal que há na tolice e na loucura das maluquices.
Saboda haka na mai da hankalina ga fahimi, don in bincika in nemi hikima da yadda aka tsara abubuwa, in kuma fahimci wawancin mugunta da haukar wauta.
26 E eu encontrei uma coisa mais amarga que a morte: a mulher cujo coração são redes e armadilhas, e suas mãos são amarras; quem for bom perante Deus escapará dela; mas o pecador ficará preso nela.
Sai na iske wani abin da ya fi mutuwa ɗaci mace wadda take tarko ne, wadda zuciyarta tarko ne wadda kuma hannuwanta sarƙa ne. Mutumin da ya gamshi Allah zai tsere mata, amma za tă kama mai zunubi.
27 Olha isto: (diz o pregador, enquanto ele procurava entender [as coisas], uma por uma)
Malami ya ce, “Duba, abin da na gane ke nan. “Na tara abu guda da wani, don in gane tsarin abubuwa,
28 Aquilo que minha alma tem buscado, ainda não achei; um homem entre mil eu achei; mas uma mulher entre todas estas não achei.
yayinda nake cikin nema amma ban samu ba, sai na sami adali guda cikin dubu, amma ba mace mai adalci guda a cikinsu duka.
29 Eis que somente achei isto: que Deus fez os homens corretos, porém foram eles que buscaram muitos desejos ruins.
Wannan ne kaɗai abin da na gane. Allah ya yi mutum tsab amma sai muka rikitar da kanmu.”

< Eclesiastes 7 >