< Zacarias 8 >

1 Depois veio a mim a palavra do Senhor dos exércitos, dizendo:
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
2 Assim diz o Senhor dos exércitos: Zelei por Sião com grande zelo, e com grande furor zelei por ela.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
3 Assim diz o Senhor: Voltarei para Sião, e habitarei no meio de Jerusalém; e Jerusalém chamar-se-á a cidade de verdade, e o monte do Senhor dos exércitos monte de santidade.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
4 Assim diz o Senhor dos exércitos: Ainda nas praças de Jerusalém habitarão velhos e velhas; e cada um terá na sua mão o seu bordão, por causa da sua muita idade.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
5 E as ruas da cidade serão cheias de meninos e meninas, que brincarão nas ruas dela.
Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
6 Assim diz o Senhor dos exércitos: Se isto será maravilhoso aos olhos do resto deste povo naqueles dias, se-lo-á por isso também maravilhoso aos meus olhos? disse o Senhor dos exércitos.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
7 Assim diz o Senhor dos exércitos: Eis que salvarei o meu povo da terra do oriente e da terra do pôr do sol;
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
8 E tra-los-ei, e habitarão no meio de Jerusalém; e me serão por povo, e eu lhes serei a eles por Deus em verdade e em justiça.
Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
9 Assim diz o Senhor dos exércitos: Esforcem-se as vossas mãos, ó vós que nestes dias ouvistes estas palavras da boca dos profetas que estiveram no dia em que foi posto o fundamento da casa do Senhor dos exércitos, para que o templo fosse edificado.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
10 Porque antes destes dias não tem havido soldada de homens, nem soldada de bestas; nem havia paz para o que entrava nem para o que saía, por causa do inimigo, porque eu incitei a todos os homens, cada um contra o seu companheiro.
Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
11 Mas agora não me haverei eu para com o resto deste povo como nos primeiros dias, diz o Senhor dos exércitos.
Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 Porque a semente será prospera, a vide dará o seu fruto, e a terra dará a sua novidade, e os céus darão o seu orvalho; e farei que o resto deste povo herde tudo isto
“Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
13 E há de ser, ó casa de Judá, e ó casa de Israel, que, assim como fostes uma maldição entre as nações, assim vos salvarei, e sereis uma benção: não temais, esforcem-se as vossas mãos.
Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
14 Porque assim diz o Senhor dos exércitos: Assim como pensei fazer-vos mal, quando vossos pais me provocaram à ira, diz o Senhor dos exércitos, e não me arrependi,
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
15 Assim tornei a pensar de fazer bem a Jerusalém e à casa de Judá, nestes dias: não temais.
kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
16 Estas são as coisas que fareis: falai verdade cada um com o seu companheiro; julgai verdade e juízo de paz nas vossas portas.
Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
17 E nenhum de vós pense mal no seu coração contra o seu companheiro, nem ameis o juramento falso; porque todas estas coisas são as que eu aborreço, diz o Senhor.
kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
18 E a palavra do Senhor dos exércitos veio a mim, dizendo:
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
19 Assim diz o Senhor dos exércitos: O jejum do quarto, e o jejum do quinto, e o jejum do sétimo, e o jejum do décimo mês se tornará para a casa de Judá em gozo, e em alegria, e em festividades solenes: amai pois a verdade e a paz.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
20 Assim diz o Senhor dos exércitos: Ainda sucederá que virão os povos e os habitantes de muitas cidades.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
21 E os habitantes de uma irão à outra, dizendo: Vamos andando para suplicar a face do Senhor, e para buscar ao Senhor dos exércitos; eu também irei.
mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
22 Assim virão muitos povos e poderosas nações, a buscar em Jerusalém ao Senhor dos exércitos, e a suplicar a face do Senhor.
Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
23 Assim diz o Senhor dos exércitos: naquele dia sucederá que pegarão dez homens de entre todas as línguas das nações, pegarão, digo, da aba de um homem judaico, dizendo: Iremos convosco, porque temos ouvido que Deus está convosco.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”

< Zacarias 8 >