< Zacarias 6 >

1 E outra vez levantei os meus olhos, e olhei, e eis que vi quatro carros que sairam dentre dois montes, e estes montes eram montes de metal.
Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
2 No primeiro carro eram cavalos vermelhos, e no segundo carro cavalos pretos,
Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
3 E no terceiro carro cavalos brancos, e no quarto carro cavalos saraivados, que eram fortes.
ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
4 E respondi, e disse ao anjo que falava comigo: Que é isto, Senhor meu?
Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
5 E o anjo respondeu, e me disse: Estes são os quatro ventos do céu, saindo de onde estavam perante o Senhor de toda a terra.
Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
6 O carro em que estão os cavalos pretos, sai para a terra do norte, e os brancos saem atráz deles, e os saraivados saem para a terra do sul.
Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
7 E os cavalos fortes saiam, e procuravam ir por diante, para andarem pela terra. E ele disse: Ide, andai pela terra. E andavam pela terra.
Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
8 E me chamou, e me falou, dizendo: Eis que aqueles que sairam para a terra do norte fizeram repousar o meu espírito na terra do norte.
Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
9 E a palavra do Senhor veio a mim, dizendo:
Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
10 Toma dos que foram levados cativos: de Heldai, de Tobias, e de Jedaia (e vem naquele dia, e entra na casa de Josias, filho de Sofonias), os quais vieram de Babilônia.
“Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
11 Toma, digo, prata e ouro, e faze corôas, e põe-as na cabeça de Josué, filho de Josadac, sumo sacerdote.
Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
12 E fala-lhe, dizendo: Assim fala o Senhor dos exércitos, dizendo: Eis aqui o homem cujo nome é o Renovo que brotará do seu lugar, e edificará o templo do Senhor.
Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
13 Ele mesmo edificará o templo do Senhor, e levará ele a glória, e assentar-se-á, e dominará no seu trono, e será sacerdote no seu trono, e conselho de paz haverá entre eles ambos.
Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
14 E estas corôas serão de Helem, e de Tobias, e de Jedaia, e de Chen, filho de Sofonias, por memorial no templo do Senhor.
Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
15 E aqueles que estão longe virão, e edificarão no templo do Senhor, e vós sabereis que o Senhor dos exércitos me tem enviado a vós; e isto acontecerá assim, se ouvirdes mui atentos a voz do Senhor vosso Deus.
Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”

< Zacarias 6 >