< Salmos 99 >
1 O Senhor reina; tremam as nações: está assentado entre os cherubins; comova-se a terra.
Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
2 O Senhor é grande em Sião, e mais alto do que todas as nações.
Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
3 Louvem o teu nome, grande e tremendo, pois é santo.
Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
4 Também o poder do Rei ama o juízo: tu firmas a equidade, fazes juízo e justiça em Jacob.
Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
5 Exaltai ao Senhor nosso Deus, e prostrai-vos diante do escabelo de seus pés, pois é santo.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
6 Moisés e Aarão, entre os seus sacerdotes, e Samuel entre os que invocam o seu nome, clamavam ao Senhor, e ele os ouvia.
Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
7 Na coluna de nuvem lhes falava: eles guardavam os seus testemunhos, e os estatutos que lhes dera.
Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
8 Tu os escutaste, Senhor nosso Deus: tu foste um Deus que lhes perdoaste, ainda que tomaste vingança dos seus feitos.
Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
9 Exaltai ao Senhor nosso Deus e adorai-o no seu monte santo, pois o Senhor nosso Deus é santo.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.