< Salmos 89 >

1 As benignidades do Senhor cantarei perpetuamente: com a minha boca manifestarei a tua fidelidade de geração em geração.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Pois disse eu: A tua benignidade será edificada para sempre: tu confirmarás a tua fidelidade até nos céus, dizendo:
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 Fiz um concerto com o meu escolhido: jurei ao meu servo David, dizendo:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 A tua semente estabelecerei para sempre, e edificarei o teu trono de geração em geração (Selah)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 E os céus louvarão as tuas maravilhas, ó Senhor, a tua fidelidade também na congregação dos santos.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Pois quem no céu se pode igualar ao Senhor? Quem entre os filhos dos poderosos pode ser semelhante ao Senhor?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 Deus é muito formidável na assembléia dos santos, e para ser reverenciado por todos os que o cercam.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 Ó Senhor, Deus dos exércitos, quem é forte como tu, Senhor? pois a tua fidelidade está à roda de ti?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Tu dominas o ímpeto do mar: quando as suas ondas se levantam, tu as fazes aquietar.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Tu quebrantaste a Rahab como se fôra ferida de morte; espalhaste os teus inimigos com o teu braço forte.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Teus são os céus, e tua é a terra; o mundo e a sua plenitude tu os fundaste.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 O norte e o sul tu os criaste; Tabor e Hermon jubilam em teu nome.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Tu tens um braço poderoso; forte é a tua mão, e alta está a tua dextra.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Justiça e juízo são o assento do teu trono, misericórdia e verdade irão adiante do teu rosto.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Bem-aventurado o povo que conhece o som alegre: andará, ó Senhor, na luz da tua face.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 Em teu nome se alegrará todo o dia, e na tua justiça se exaltará.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Pois tu és a glória da sua força; e no teu favor será exaltado o nosso poder.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Porque o Senhor é a nossa defesa, e o Santo de Israel o nosso Rei.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Então falaste em visão ao teu santo, e disseste: pus o socorro sobre um que é poderoso: exaltei a um eleito do povo.
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 Achei a David, meu servo; com santo óleo o ungi:
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 Com o qual a minha mão ficará firme, e o meu braço o fortalecerá.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 O inimigo não apertará com ele, nem o filho da perversidade o afligirá.
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 E eu derribarei os seus inimigos perante a sua face, e ferirei aos que o aborrecem.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 E a minha fidelidade e a minha benignidade estarão com ele; e em meu nome será exaltado o seu poder.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Porei também a sua mão no mar, e a sua direita nos rios.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Ele me chamará, dizendo: Tu és meu Pai, meu Deus, e a rocha da minha salvação.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Também o farei meu primogênito, mais elevado do que os reis da terra.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 A minha benignidade lhe conservarei eu para sempre, e o meu concerto lhe será firme.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 E conservarei para sempre a sua semente, e o seu trono como os dias do céu.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Se os seus filhos deixarem a minha lei, e não andarem nos meus juízos,
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 Se profanarem os meus preceitos, e não guardarem os meus mandamentos,
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 Então visitarei a sua transgressão com a vara, e a sua iniquidade com açoites.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Porém não retirarei totalmente dele a minha benignidade, nem faltarei à minha fidelidade.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 Não quebrarei o meu concerto, não alterarei o que saiu dos meus lábios.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 Uma vez jurei pela minha santidade que não mentirei a David.
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 A sua semente durará para sempre, e o seu trono, como o sol diante de mim,
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Será estabelecido para sempre como a lua, e como uma testemunha fiel no céu (Selah)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Porém tu rejeitaste e aborreceste; tu te indignaste contra o teu ungido.
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Abominaste o concerto do teu servo: profanaste a sua coroa, lançando-a por terra.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Derrubaste todos os seus valados; arruinaste as suas fortificações.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Todos os que passam pelo caminho o despojam; é um opróbrio para os seus vizinhos.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Exaltaste a dextra dos seus adversários; fizeste com que todos os seus inimigos se regozijassem.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Também embotaste os fios da sua espada, e não o sustentaste na peleja.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Fizeste cessar a sua glória, e deitaste por terra o seu trono.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Abreviaste os dias da sua mocidade; cobriste-o de vergonha (Selah)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Até quando, Senhor? Acaso te esconderás para sempre? arderá a tua ira como fogo?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Lembra-te de quão breves são os meus dias; pelo que debalde criaste todos os filhos dos homens.
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Que homem há, que viva, e não veja a morte? Livrará ele a sua alma do poder da sepultura? (Selah) (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Senhor, onde estão as tuas antigas benignidades, que juraste a David pela tua verdade?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Lembra-te, Senhor, do opróbrio dos teus servos; como eu trago no meu peito o opróbrio de todos os povos poderosos:
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 Com o qual, Senhor, os teus inimigos tem difamado, com o qual tem difamado as pisadas do teu ungido.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Bendito seja o Senhor para sempre. amém, e amém.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Salmos 89 >