< Salmos 89 >
1 As benignidades do Senhor cantarei perpetuamente: com a minha boca manifestarei a tua fidelidade de geração em geração.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Pois disse eu: A tua benignidade será edificada para sempre: tu confirmarás a tua fidelidade até nos céus, dizendo:
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 Fiz um concerto com o meu escolhido: jurei ao meu servo David, dizendo:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 A tua semente estabelecerei para sempre, e edificarei o teu trono de geração em geração (Selah)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 E os céus louvarão as tuas maravilhas, ó Senhor, a tua fidelidade também na congregação dos santos.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Pois quem no céu se pode igualar ao Senhor? Quem entre os filhos dos poderosos pode ser semelhante ao Senhor?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 Deus é muito formidável na assembléia dos santos, e para ser reverenciado por todos os que o cercam.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 Ó Senhor, Deus dos exércitos, quem é forte como tu, Senhor? pois a tua fidelidade está à roda de ti?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Tu dominas o ímpeto do mar: quando as suas ondas se levantam, tu as fazes aquietar.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Tu quebrantaste a Rahab como se fôra ferida de morte; espalhaste os teus inimigos com o teu braço forte.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Teus são os céus, e tua é a terra; o mundo e a sua plenitude tu os fundaste.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 O norte e o sul tu os criaste; Tabor e Hermon jubilam em teu nome.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Tu tens um braço poderoso; forte é a tua mão, e alta está a tua dextra.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Justiça e juízo são o assento do teu trono, misericórdia e verdade irão adiante do teu rosto.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Bem-aventurado o povo que conhece o som alegre: andará, ó Senhor, na luz da tua face.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 Em teu nome se alegrará todo o dia, e na tua justiça se exaltará.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Pois tu és a glória da sua força; e no teu favor será exaltado o nosso poder.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Porque o Senhor é a nossa defesa, e o Santo de Israel o nosso Rei.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Então falaste em visão ao teu santo, e disseste: pus o socorro sobre um que é poderoso: exaltei a um eleito do povo.
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 Achei a David, meu servo; com santo óleo o ungi:
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 Com o qual a minha mão ficará firme, e o meu braço o fortalecerá.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 O inimigo não apertará com ele, nem o filho da perversidade o afligirá.
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 E eu derribarei os seus inimigos perante a sua face, e ferirei aos que o aborrecem.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 E a minha fidelidade e a minha benignidade estarão com ele; e em meu nome será exaltado o seu poder.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Porei também a sua mão no mar, e a sua direita nos rios.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Ele me chamará, dizendo: Tu és meu Pai, meu Deus, e a rocha da minha salvação.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Também o farei meu primogênito, mais elevado do que os reis da terra.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 A minha benignidade lhe conservarei eu para sempre, e o meu concerto lhe será firme.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 E conservarei para sempre a sua semente, e o seu trono como os dias do céu.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Se os seus filhos deixarem a minha lei, e não andarem nos meus juízos,
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 Se profanarem os meus preceitos, e não guardarem os meus mandamentos,
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 Então visitarei a sua transgressão com a vara, e a sua iniquidade com açoites.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Porém não retirarei totalmente dele a minha benignidade, nem faltarei à minha fidelidade.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 Não quebrarei o meu concerto, não alterarei o que saiu dos meus lábios.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 Uma vez jurei pela minha santidade que não mentirei a David.
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 A sua semente durará para sempre, e o seu trono, como o sol diante de mim,
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Será estabelecido para sempre como a lua, e como uma testemunha fiel no céu (Selah)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Porém tu rejeitaste e aborreceste; tu te indignaste contra o teu ungido.
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Abominaste o concerto do teu servo: profanaste a sua coroa, lançando-a por terra.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Derrubaste todos os seus valados; arruinaste as suas fortificações.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Todos os que passam pelo caminho o despojam; é um opróbrio para os seus vizinhos.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Exaltaste a dextra dos seus adversários; fizeste com que todos os seus inimigos se regozijassem.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Também embotaste os fios da sua espada, e não o sustentaste na peleja.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Fizeste cessar a sua glória, e deitaste por terra o seu trono.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Abreviaste os dias da sua mocidade; cobriste-o de vergonha (Selah)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Até quando, Senhor? Acaso te esconderás para sempre? arderá a tua ira como fogo?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Lembra-te de quão breves são os meus dias; pelo que debalde criaste todos os filhos dos homens.
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Que homem há, que viva, e não veja a morte? Livrará ele a sua alma do poder da sepultura? (Selah) (Sheol )
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
49 Senhor, onde estão as tuas antigas benignidades, que juraste a David pela tua verdade?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Lembra-te, Senhor, do opróbrio dos teus servos; como eu trago no meu peito o opróbrio de todos os povos poderosos:
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 Com o qual, Senhor, os teus inimigos tem difamado, com o qual tem difamado as pisadas do teu ungido.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Bendito seja o Senhor para sempre. amém, e amém.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!