< Salmos 83 >

1 Ó Deus, não estejas em silêncio; não te cales, nem te aquietes, ó Deus.
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Porque eis que teus inimigos fazem tumulto, e os que te aborrecem levantaram a cabeça.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 Tomaram astuto conselho contra o teu povo, e consultavam contra os teus escondidos.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 Disseram: Vinde, e desarreiguemo-los para que não sejam nação, nem haja mais memória do nome de Israel.
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Porque consultaram juntos e unânimes; eles se aliam contra ti:
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 As tendas de Edom, e dos ismaelitas, de Moab, e dos agarenos,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 De Gebal, e de Ammon, e de Amalek, de Palestina, com os moradores de Tiro.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Também Assyria se ajuntou com eles: foram ajudar aos filhos de Lot (Selah)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Faze-lhes como aos madianitas; como a Sisera, como a Jabin na ribeira de Kison.
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Os quais pereceram em Endor; tornaram-se como estrume para a terra.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Faze aos seus nobres como a Oreb, e como a Zeeb e a todos os seus príncipes, como a Zebah e como a Zalmuna;
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 Que disseram: Tomemos para nós as casas de Deus em possessão.
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Deus meu, faze-os como um tufão, como a aresta diante do vento.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Como o fogo que queima um bosque, e como a chama que incendeia as brenhas,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 Assim os persegue com a tua tempestade, e os assombra com o teu torvelinho.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Encham-se de vergonha as suas faces, para que busquem o teu nome, Senhor.
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Confundam-se e assombrem-se perpetuamente; envergonhem-se, e pereçam.
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 Para que saibam que tu, a quem só pertence o nome de Jehovah, és o altíssimo sobre toda a terra.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.

< Salmos 83 >