< Salmos 75 >

1 A ti, ó Deus, glorificamos, a ti damos louvor, pois o teu nome está perto, as tuas maravilhas o declaram.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
2 Quando eu ocupar o lugar determinado, julgarei retamente.
Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
3 A terra e todos os seus moradores estão dissolvidos, mas eu fortaleci as suas colunas (Selah)
Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
4 Disse eu aos loucos: Não enlouqueçais; e aos ímpios: Não levanteis a fronte:
Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
5 Não levanteis a vossa fronte altiva, nem faleis com cerviz dura;
Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
6 Porque nem do oriente, nem do ocidente, nem do deserto vem a exaltação.
Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
7 Mas Deus é o Juiz; a um abate, e a outro exalta.
Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
8 Porque na mão do Senhor há um cálice, cujo vinho é roxo; está cheio de mistura; e dá a beber dele; mas as fezes dele todos os ímpios da terra as sorverão e beberão.
A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
9 E eu o declararei para sempre; cantarei louvores ao Deus de Jacob.
Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
10 E quebrarei todas as forças dos ímpios, mas as forças dos justos serão exaltadas.
wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”

< Salmos 75 >