< Salmos 69 >

1 Livra-me, ó Deus, pois as águas entraram até à minha alma.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 Atolei-me em profundo lamaçal, onde se não pode estar em pé; entrei na profundeza das águas, onde a corrente me leva.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 Estou cançado de clamar; a minha garganta se secou: os meus olhos desfalecem esperando o meu Deus.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 Aqueles que me aborrecem sem causa são mais do que os cabelos da minha cabeça; aqueles que procuram destruir-me, sendo injustamente meus inimigos, são poderosos: então restitui o que não furtei.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 Tu, ó Deus, bem conheces a minha insipiência; e os meus pecados não te são encobertos.
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 Não sejam envergonhados por minha causa aqueles que esperam em ti, ó Senhor, Senhor dos exércitos; não sejam confundidos por minha causa aqueles que te buscam, ó Deus de Israel.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 Porque por amor de ti tenho suportado afrontas; a confusão cobriu o meu rosto.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 Tenho-me tornado um estranho para com meus irmãos, e um desconhecido para com os filhos de minha mãe.
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 Pois o zelo da tua casa me devorou, e as afrontas dos que te afrontam cairam sobre mim.
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 Quando chorei, e castiguei com jejum a minha alma, isto se me tornou em afrontas.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 Pus por vestido um saco, e me fiz um provérbio para eles.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 Aqueles que se assentam à porta falam contra mim; e fui o cântico dos bebedores de bebida forte.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 Eu porém faço a minha oração a ti, Senhor, num tempo acceitável: ó Deus, ouve-me segundo a grandeza da tua misericórdia, segundo a verdade da tua salvação.
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Tira-me do lamaçal, e não me deixes atolar; seja eu livre dos que me aborrecem, e das profundezas das águas.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 Não me leve a corrente das águas, e não me absorva ao profundo, nem o poço cerre a sua boca sobre mim.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Ouve-me, Senhor, pois boa é a tua misericórdia: olha para mim segundo a tua muitíssima piedade.
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 E não escondas o teu rosto do teu servo, porque estou angustiado: ouve-me depressa.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Aproxima-te da minha alma, e resgata-a; livra-me por causa dos meus inimigos.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 Bem tens conhecido a minha afronta, e a minha vergonha, e a minha confusão; diante de ti estão todos os meus adversários.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 Afrontas me quebrantaram o coração, e estou fraquíssimo: esperei por alguém que tivesse compaixão, mas não houve nenhum; e por consoladores, mas não os achei.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 Deram-me fel por mantimento, e na minha sede me deram a beber vinagre.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 Torne-se-lhes a sua mesa diante deles em laço e para sua recompensa em ruína.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Escureçam-se-lhes os seus olhos, para que não vejam, e faze com que os seus lombos tremam constantemente.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Derrama sobre eles a tua indignação, e prenda-os o ardor da tua ira.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 Fique desolado o seu palácio; e não haja quem habite nas suas tendas.
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 Pois perseguem àquele a quem feriste, e conversam sobre a dor daqueles a quem chagaste.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Acrescenta iniquidade à iniquidade deles, e não entrem na tua justiça.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 Sejam riscados do livro dos vivos, e não sejam escritos com os justos.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 Eu porém sou pobre, e estou triste: ponha-me a tua salvação, ó Deus, num alto retiro.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 Louvarei o nome de Deus com um cântico, e engrandece-lo-ei com ação de graças.
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 Isto será mais agradável ao Senhor do que o boi ou bezerro que tem pontas e unhas.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 Os mansos verão isto, e se agradarão; o vosso coração viverá, pois que buscais a Deus
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 Porque o Senhor ouve os necessitados, e não despreza os seus cativos.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 Louvem-no os céus e a terra, os mares e tudo quanto neles se move.
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 Porque Deus salvará a Sião, e edificará as cidades de Judá, para que habitem nela e as possuam.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 E herda-la-á a semente de seus servos, e os que amam o seu nome habitarão nela.
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< Salmos 69 >