< Salmos 36 >
1 A prevaricação do ímpio diz no intimo do seu coração: Não há temor de Deus perante os seus olhos.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
2 Porque em seus olhos se lisongeia, até que a sua iniquidade se descubra ser detestável.
Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
3 As palavras da sua boca são malícia e engano: deixou de entender e de fazer o bem.
Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
4 Projeta a malícia na sua cama; põe-se no caminho que não é bom: não aborrece o mal
Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
5 A tua misericórdia, Senhor, está nos céus, e a tua fidelidade chega até às mais excelsas nuvens.
Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
6 A tua justiça é como as grandes montanhas; os teus juízos são um grande abismo; Senhor, tu conservas os homens e os animais.
Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
7 Quão preciosa é, ó Deus, a tua benignidade, pelo que os filhos dos homens se abrigam à sombra das tuas asas.
Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
8 Eles se fartarão da gordura da tua casa, e os farás beber da corrente das tuas delícias;
Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
9 Porque em ti está o manancial da vida; na tua luz veremos a luz.
Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
10 Estende a tua benignidade sobre os que te conhecem, e a tua justiça sobre os retos de coração.
Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
11 Não venha sobre mim o pé dos soberbos, e não me mova a mão dos ímpios.
Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
12 Ali caem os que obram a iniquidade; cairão, e não se poderão levantar.
Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!