< Salmos 145 >
1 Eu te exaltarei, ó Deus, rei meu, e bendirei o teu nome pelo século do século e para sempre.
Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
2 Cada dia te bendirei, e louvarei o teu nome pelo século do século e para sempre.
Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
3 Grande é o Senhor, e muito digno de louvor, e a sua grandeza inexcrutável.
Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
4 Uma geração louvará as tuas obras à outra geração, e anunciarão as tuas proezas.
Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
5 Falarei da magnificência gloriosa da tua magestade e das tuas obras maravilhosas.
Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
6 E se falará da força dos teus feitos terríveis; e contarei a tua grandeza.
Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
7 Proferirão abundantemente a memória da tua grande bondade, e cantarão a tua justiça.
Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
8 Piedoso e benigno é o Senhor, sofredor e de grande misericórdia.
Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
9 O Senhor é bom para todos, e as suas misericórdias são sobre todas as suas obras.
Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
10 Todas as tuas obras te louvarão, ó Senhor, e os teus santos te bendirão.
Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
11 Falarão da glória do teu reino, e relatarão o teu poder,
Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
12 Para fazer saber aos filhos dos homens as tuas proezas e a glória da magnificência do teu reino.
saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
13 O teu reino é um reino eterno; o teu domínio dura em todas as gerações.
Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
14 O Senhor sustenta a todos os que caem, e levanta a todos os abatidos.
Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
15 Os olhos de todos esperam em ti, e lhes dás o seu mantimento a seu tempo.
Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
16 Abres a tua mão, e fartas os desejos de todos os viventes.
Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
17 Justo é o Senhor em todos os seus caminhos, e santo em todas as suas obras.
Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
18 Perto está o Senhor de todos os que o invocam, de todos os que o invocam em verdade.
Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
19 Ele cumprirá o desejo dos que o temem; ouvirá o seu clamor, e os salvará.
Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
20 O Senhor guarda a todos os que o amam; porém todos os ímpios serão destruídos.
Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
21 A minha boca falará o louvor do Senhor, e toda a carne louvará o seu santo nome pelo século do século e para sempre.
Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.