< Salmos 116 >

1 Amo ao Senhor, porque ele ouviu a minha voz e a minha súplica.
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 Porque inclinou a mim os seus ouvidos; portanto o invocarei enquanto viver.
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 Os cordeis da morte me cercaram, e angústias do inferno se apoderaram de mim: encontrei aperto e tristeza. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
4 Então invoquei o nome do Senhor, dizendo: Ó Senhor, livra a minha alma.
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 Piedoso é o Senhor e justo: o nosso Deus tem misericórdia.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 O Senhor guarda aos símplices: fui abatido, mas ele me livrou.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Alma minha, volta para o teu repouso, pois o Senhor te fez bem.
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 Porque tu, Senhor, livraste a minha alma da morte, os meus olhos das lágrimas, e os meus pés da queda.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 Andarei perante a face do Senhor na terra dos viventes.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 Cri, por isso falei: estive muito aflito.
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 Dizia na minha pressa: Todos os homens são mentirosos.
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 Que darei eu ao Senhor, por todos os benefícios que me tem feito?
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 Tomarei o cálice da salvação, e invocarei o nome do Senhor.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 Pagarei os meus votos ao Senhor, agora, na presença de todo o seu povo.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 Preciosa é à vista do Senhor a morte dos seus santos.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 Ó Senhor, deveras sou teu servo: sou teu servo, filho da tua serva; soltaste as minhas ataduras.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 Oferecer-te-ei sacrifícios de louvor, e invocarei o nome do Senhor.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 Pagarei os meus votos ao Senhor, na presença de todo o meu povo.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 Nos átrios da casa do Senhor, no meio de ti, ó Jerusalém. louvai ao Senhor.
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Salmos 116 >