< Salmos 102 >
1 Senhor, ouve a minha oração, e chegue a ti o meu clamor.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Não escondas de mim o teu rosto no dia da minha angústia, inclina para mim os teus ouvidos; no dia em que eu clamar, ouve-me depressa.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Porque os meus dias se consomem como o fumo, e os meus ossos ardem como um lar.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 O meu coração está ferido e seco como a erva, pelo que me esqueço de comer o meu pão
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Por causa da voz do meu gemido os meus ossos se apegam à minha pele.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Sou semelhante ao pelicano no deserto: sou como um mocho nas solidões.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Vigio, sou como o pardal solitário no telhado.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Os meus inimigos me afrontam todo o dia: os que se enfurecem contra mim tem jurado.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Pois tenho comido cinza como pão, e misturado com lágrimas a minha bebida.
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 Por causa da tua ira e da tua indignação, pois tu me levantaste e me arremeçaste.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Os meus dias são como a sombra que declina, e como a erva me vou secando.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Mas tu, Senhor, permanecerás para sempre, e a tua memória de geração em geração.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Tu te levantarás e terás piedade de Sião; pois o tempo de te compadeceres dela, o tempo determinado, já chegou.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Porque os teus servos tem prazer nas suas pedras, e se compadecem do seu pó.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Então as nações temerão o nome do Senhor, e todos os reis da terra a tua glória.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 Quando o Senhor edificar a Sião, aparecerá na sua glória.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Ele atenderá à oração do desamparado, e não desprezará a sua oração.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Isto se escreverá para a geração futura; e o povo que se criar louvará ao Senhor.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 Pois olhou desde o alto do seu santuário, desde os céus o Senhor contemplou a terra.
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 Para ouvir o gemido dos presos, para soltar os sentenciados à morte;
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 Para anunciarem o nome do Senhor em Sião, e o seu louvor em Jerusalém;
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 Quando os povos se ajuntarem, e os reinos, para servirem ao Senhor.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Abateu a minha força no caminho; abreviou os meus dias.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Dizia eu: Meu Deus, não me leves no meio dos meus dias, os teus anos são por todas as gerações.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Desde a antiguidade fundaste a terra: e os céus são obra das tuas mãos.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Eles perecerão, mas tu permanecerás: todos eles se envelhecerão como um vestido; como roupa os mudarás, e ficarão mudados.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Porém tu és o mesmo, e os teus anos nunca terão fim.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Os filhos dos teus servos continuarão, e a sua semente ficará firmada perante ti.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”