< Provérbios 8 >

1 Não clama porventura a sabedoria, e a inteligência não dá a sua voz?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 No cume das alturas, junto ao caminho, nas encruzilhadas das veredas se põe.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Da banda das portas da cidade, à entrada da cidade, e à entrada das portas está gritando.
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 A vós, ó homens, clamo; e a minha voz se dirige aos filhos dos homens.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Entendei, ó símplices, a prudência: e vós, loucos, entendei do coração.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Ouvi, porque falarei coisas excelentes: os meus lábios se abrirão para a equidade.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Porque a minha boca proferirá a verdade, e os meus lábios abominam a impiedade.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Em justiça estão todas as palavras da minha boca: não há nelas nenhuma coisa tortuosa nem perversa.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Todas elas são retas para o que bem as entende, e justas para os que acham o conhecimento.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Aceitai a minha correção, e não a prata: e o conhecimento, mais do que o ouro fino escolhido.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Porque melhor é a sabedoria do que os rubins; e tudo o que mais se deseja não se pode comparar com ela.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Eu, a sabedoria, habito com a prudência, e acho a ciência dos conselhos.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 O temor do Senhor é aborrecer o mal: a soberba, e a arrogância, e o mau caminho, e a boca perversa, aborreço.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Meu é o conselho e verdadeira sabedoria: eu sou o entendimento, minha é a fortaleza.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Por mim reinam os reis e os príncipes ordenam justiça.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Por mim dominam os dominadores, e príncipes, todos os juízes da terra.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 Eu amo aos que me amam, e os que de madrugada me buscam me acharão.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Riquezas e honra estão comigo; como também opulência durável e justiça.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Melhor é o meu fruto do que o fino ouro e do que o ouro refinado, e as minhas novidades do que a prata escolhida.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Faço andar pelo caminho da justiça, no meio das veredas do juízo.
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 Para que faça herdar bens permanentes aos que me amam, e eu encha os seus tesouros.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 O Senhor me possuiu no princípio de seus caminhos, desde então, e antes de suas obras.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 Desde a eternidade fui ungida, desde o princípio, antes do começo da terra.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Quando ainda não havia abismos, fui gerada, quando ainda não havia fontes carregadas de águas.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Antes que os montes se houvessem assentado, antes dos outeiros, eu era gerada.
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 Ainda não tinha feito a terra, nem os campos, nem o princípio dos mais miúdos do mundo.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Quando preparava os céus, ai estava eu, quando compassava ao redor a face do abismo,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 Quando afirmava as nuvens de cima, quando fortificava as fontes do abismo,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 Quando punha ao mar o seu termo, para que as águas não trespassassem o seu mando, quando compunha os fundamentos da terra.
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 Então eu estava com ele por aluno: e eu era cada dia as suas delícias, folgando perante ele em todo o tempo;
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 Folgando no seu mundo habitável, e achando as minhas delícias com os filhos dos homens.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Agora, pois, filhos, ouvi-me, porque bem-aventurados serão os que guardarem os meus caminhos.
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Ouvi a correção, e sede sábios, e não a rejeiteis.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Bem-aventurado o homem que me dá ouvidos, velando às minhas portas cada dia, esperando às hombreiras das minhas entradas.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Porque o que me achar achará a vida, e alcançará favor do Senhor.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Mas o que pecar contra mim violentará a sua própria alma: todos os que me aborrecem amam a morte.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Provérbios 8 >