< Provérbios 6 >

1 Filho meu, se ficaste por fiador do teu companheiro, se deste a tua mão ao estranho,
Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
2 Enredaste-te com as palavras da tua boca: prendeste-te com as palavras da tua boca.
in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
3 Faze pois isto agora, filho meu, e livra-te, pois já caíste nas mãos do teu companheiro; vai, humilha-te, e aperta com o teu companheiro.
to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
4 Não dês sono aos teus olhos, nem adormecimento às tuas pálpebras.
Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
5 Livra-te como o corço da mão do passarinheiro.
Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
6 Vai-te à formiga, ó preguiçoso: olha para os seus caminhos, e sê sábio.
Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
7 A qual, não tendo superior, nem oficial, nem dominador,
Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
8 Prepara no verão o seu pão: na sega ajunta o seu mantimento.
duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
9 Oh! preguiçoso, até quando ficarás deitado? quando te levantarás do teu sono?
Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
10 Um pouco de sono, um pouco tosquenejando; um pouco encruzando as mãos, para estar deitado.
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
11 Assim te sobrevirá a tua pobreza como o caminhante, e a tua necessidade como um homem armado.
talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
12 O homem de Belial, o homem vicioso, anda em perversidade de boca.
Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
13 Acena com os olhos, fala com os pés, ensina com os dedos.
wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
14 Perversidade há no seu coração, todo o tempo maquina mal: anda semeando contendas.
wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
15 Pelo que a sua destruição virá repentinamente: subitamente será quebrantado, sem que haja cura.
Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
16 Estas seis coisas aborrece o Senhor, e sete a sua alma abomina:
Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
17 Olhos altivos, língua mentirosa, e mãos que derramam sangue inocente:
duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
18 O coração que maquina pensamentos viciosos; pés que se apressam a correr para o mal;
zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
19 A testemunha falsa que respira mentiras: e o que semeia contendas entre irmãos.
mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
20 Filho meu, guarda o mandamento de teu pai, e não deixes a lei de tua mãe;
Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
21 Ata-os perpetuamente ao teu coração, e pendura-os ao teu pescoço.
Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
22 Quando caminhares, te guiará; quando te deitares, te guardará; quando acordares, ela falará contigo.
Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
23 Porque o mandamento é uma lâmpada, e a lei uma luz: e as repreensões da correção são o caminho da vida
Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
24 Para te guardarem da má mulher, e das lisonjas da língua estranha.
suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
25 Não cobices no teu coração a sua formosura, nem te prendas com os seus olhos.
Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
26 Porque por causa de uma mulher prostituta se chega a pedir um bocado de pão; e a mulher dada a homens anda à caça da preciosa alma.
Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
27 Porventura tomará alguém fogo no seu seio, sem que os seus vestidos se queimem?
Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
28 Ou andará alguém sobre as brazas, sem que se queimem os seus pés?
Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
29 Assim será o que entrar à mulher do seu próximo: não ficará inocente todo aquele que a tocar.
Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
30 Não injuriam ao ladrão, quando furta, para saciar a sua alma, tendo fome;
Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
31 Mas, achado, pagará sete vezes tanto: dará toda a fazenda de sua casa.
Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
32 Porém o que adultera com uma mulher é falto de entendimento; destrói a sua alma, o que tal faz.
Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
33 Achará castigo e vilipêndio, e o seu opróbrio nunca se apagará.
Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
34 Porque ciúmes são furores do marido, e de maneira nenhuma perdoará no dia da vingança.
Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
35 Nenhum resgate aceitará, nem consentirá, ainda que aumentes os presentes.
Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.

< Provérbios 6 >