< Lucas 1 >
1 Tendo pois muitos empreendido pôr em ordem a narração das coisas que entre nós se cumpriram,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 Segundo nos transmitiram os mesmos que as viram desde o princípio, e foram ministros da palavra,
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 Pareceu-me também a mim conveniente escreve-las a ti, ó excelente Theophilo, por sua ordem, havendo-me já informado minuciosamente de tudo desde o princípio;
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 Para que conheças a certeza das coisas de que já estás informado.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 Existiu, no tempo de Herodes, rei da Judeia, um sacerdote chamado Zacarias, da ordem de Abias, e cuja mulher era das filhas de Aarão; e o seu nome era Isabel.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 E eram ambos justos perante Deus, andando sem repreensão em todos os mandamentos e preceitos do Senhor.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 E não tinham filhos, porquanto Isabel era estéril, e ambos eram avançados em idade.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 E aconteceu que, exercendo ele o sacerdócio diante de Deus, na ordem da sua turma,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 Segundo o costume sacerdotal, coube-lhe em sorte entrar no templo do Senhor a oferecer o incenso.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 E toda a multidão do povo estava fora, orando à hora do incenso,
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 E um anjo do Senhor lhe apareceu, posto em pé, à direita do altar do incenso.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 E Zacarias, vendo-o, turbou-se, e caiu temor sobre ele.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 Mas o anjo lhe disse: Zacarias, não temas, porque a tua oração foi ouvida, e Isabel, tua mulher, dará à luz um filho, e lhe porás o nome de João;
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 E terás prazer e alegria, e muitos se alegrarão no seu nascimento;
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 Porque será grande diante do Senhor, e não beberá vinho, nem bebida forte, e será cheio do Espírito Santo, até desde o ventre de sua mãe;
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 E converterá muitos dos filhos de Israel ao Senhor seu Deus;
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 E irá adiante dele no espírito e virtude de Elias, para converter os corações dos pais aos filhos, e os rebeldes à prudência dos justos; para preparar ao Senhor um povo bem disposto.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 Disse então Zacarias ao anjo: Como conhecerei isto? pois eu já sou velho, e minha mulher avançada em idade.
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 E, respondendo o anjo, disse-lhe: Eu sou Gabriel, que assisto diante de Deus, e fui enviado a falar-te e dar-te estas alegres novas;
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 E eis que ficarás mudo, e não poderás falar até ao dia em que estas coisas aconteçam; porquanto não creeste nas minhas palavras, que a seu tempo se hão de cumprir
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 E o povo estava esperando a Zacarias, e maravilhavam-se de que tanto se demorasse no templo.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 E, saindo ele, não lhes podia falar; e entenderam que tinha visto alguma visão no templo. E falava por acenos, e ficou mudo.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 E sucedeu que, terminados os dias do seu ministério, voltou para sua casa.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 E depois daqueles dias Isabel, sua mulher, concebeu, e por cinco meses se ocultou, dizendo:
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 Porque isto me fez o Senhor, nos dias em que atentou em mim, para destruir o meu opróbrio entre os homens.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 E, no sexto mes, foi o anjo Gabriel enviado por Deus a uma cidade da Galiléia, chamada Nazareth,
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 A uma virgem desposada com um varão, cujo nome era José, da casa de David; e o nome da virgem era Maria.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 E, entrando o anjo aonde ela estava, disse: Salve, agraciada; o Senhor é contigo: bendita tu entre as mulheres.
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 E, vendo-o ela, turbou-se muito das suas palavras, e considerava que saudação seria esta.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 Disse-lhe então o anjo: Maria, não temas, porque achaste graça diante de Deus;
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 E eis que em teu ventre conceberás, e darás à luz um filho, e pôr-lhe-as o nome de Jesus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 Este será grande, e será chamado filho do altíssimo; e o Senhor Deus lhe dará o trono de David, seu pai;
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 E reinará eternamente na casa de Jacob, e o seu reino não terá fim. (aiōn )
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
34 E disse Maria ao anjo: Como se fará isto? pois não conheço varão.
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 E, respondendo o anjo, disse-lhe: Descerá sobre ti o Espírito Santo, e a virtude do altíssimo te cobrirá com a sua sombra; pelo que também o Santo, que de ti há de nascer, será chamado Filho de Deus.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 E eis que também Isabel, tua prima, concebeu um filho em sua velhice; e é este o sexto mês para aquela que era chamada estéril;
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 Porque para Deus nada será impossível.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 Disse então Maria: Eis aqui a serva do Senhor; cumpra-se em mim segundo a tua palavra. E o anjo ausentou-se dela.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 E naqueles dias, levantando-se Maria, foi apressada às montanhas, a uma cidade de Juda,
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 E entrou em casa de Zacarias, e saudou a Isabel.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 E aconteceu que, ao ouvir Isabel a saudação de Maria, a criancinha saltou no seu ventre; e Isabel foi cheia do Espírito Santo,
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 E exclamou com grande voz, e disse: bendita tu entre as mulheres, e bendito o fruto do teu ventre.
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 E de onde me provém isto a mim, que a mãe do meu Senhor venha a mim?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 Pois eis que, ao chegar aos meus ouvidos a voz da tua saudação, a criancinha saltou de alegria no meu ventre;
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 E benaventurada a que creu, pois hão de cumprir-se as coisas que da parte do Senhor lhe foram ditas.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 Disse então Maria: A minha alma engrandece ao Senhor,
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 E o meu espírito se alegra em Deus meu Salvador;
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 Porque atentou na baixeza de sua serva; pois eis que desde agora todas as gerações me chamarão benaventurada:
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 Porque me fez grandes coisas o Poderoso; e santo é o seu nome.
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 E a sua misericórdia é de geração em geração sobre os que o temem.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 Com o seu braço obrou valorosamente: dissipou os soberbos no pensamento de seus corações.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 Depôs dos tronos os poderosos, e elevou os humildes.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 Encheu de bens os famintos, e despediu vazios os ricos.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 Auxiliou a Israel seu servo, recordando-se da sua misericórdia;
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 Como falou a nossos pais, a Abraão e à sua posteridade, para sempre. (aiōn )
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
56 E Maria ficou com ela quase três meses, e depois voltou para sua casa.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 E completou-se para Isabel o tempo de dar à luz, e teve um filho.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 E os seus vizinhos e parentes ouviram que tinha Deus usado para com ela de grande misericórdia, e alegraram-se com ela.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 E aconteceu que, ao oitavo dia, vieram circuncidar o menino, e lhe chamavam Zacarias, do nome de seu pai.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 E, respondendo sua mãe, disse: Não, porém será chamado João.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 E disseram-lhe: ninguém há na tua parentela que se chame por este nome.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 E perguntaram por acenos ao pai como queria que lhe chamassem.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 E, pedindo ele uma taboinha de escrever, escreveu, dizendo: O seu nome é João. E todos se maravilharam.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 E logo a boca se lhe abriu, e a língua se lhe soltou; e falava, louvando a Deus.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 E veio temor sobre todos os seus circunvizinhos, e em todas as montanhas da Judeia foram divulgadas todas estas coisas.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 E todos os que as ouviam as conservavam em seus corações, dizendo: Quem será pois este menino? E a mão do Senhor estava com ele.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 E Zacarias, seu pai, foi cheio do Espírito Santo, e profetizou, dizendo:
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 Bendito o Senhor Deus de Israel, porque visitou e remiu o seu povo,
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 E nos levantou uma salvação poderosa na casa de David seu servo,
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 Como falou pela boca dos seus santos profetas, desde o princípio do mundo; (aiōn )
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
71 Que nos livraria dos nossos inimigos e da mão de todos os que nos aborrecem;
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 Para manifestar misericórdia a nossos pais, e lembrar-se do seu santo concerto,
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 E do juramento que jurou a Abraão nosso pai,
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 De conceder-nos que, libertados da mão de nossos inimigos, o serviríamos sem temor,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 Em santidade e justiça perante ele, todos os dias da nossa vida.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 E tu, ó menino, serás chamado profeta do altíssimo, porque as de ir adiante da face do Senhor, a preparar os seus caminhos;
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 Para dar ao seu povo conhecimento da salvação, na remissão dos seus pecados;
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 Pelas entranhas da misericórdia do nosso Deus, com que o Oriente do alto nos visitou;
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 Para alumiar aos que estão assentados em trevas e sombra de morte; a fim de dirigir os nossos pés pelo caminho da paz.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 E o menino crescia, e se robustecia em espírito. E esteve nos desertos até ao dia em que havia de mostrar-se a Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.