< Lucas 12 >

1 Ajuntando-se entretanto muitos milhares de pessoas, de sorte que se atropelavam uns aos outros, começou a dizer aos seus discípulos: acautelai-vos primeiramente do fermento dos fariseus, que é a hipocrisia.
Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
2 Mas nada há encoberto que não haja de ser descoberto; nem oculto, que não haja de ser sabido.
Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
3 Porquanto tudo o que em trevas dissestes à luz será ouvido; e o que falastes ao ouvido no gabinete sobre os telhados será apregoado.
Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
4 E digo-vos, amigos meus; Não temais os que matam o corpo, e depois não tem mais que fazer.
“Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
5 Mas eu vos mostrarei a quem deveis temer; temei aquele que, depois de matar, tem poder para lançar no inferno; sim, vos digo, a esse temei. (Geenna g1067)
Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna g1067)
6 Não se vendem cinco passarinhos por dois ceitis? E nenhum deles está esquecido diante de Deus.
Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
7 E até os cabelos da vossa cabeça estão todos contados. Não temais pois; mais valeis vós do que muitos passarinhos.
Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
8 E digo-vos que todo aquele que me confessar diante dos homens, também o Filho do homem o confessará diante dos anjos de Deus.
“Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
9 Mas quem me negar diante dos homens será negado diante dos anjos de Deus.
Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
10 E a todo aquele que disser uma palavra contra o Filho do homem ser-lhe-á perdoada, mas ao que blasfemar contra o Espírito Santo não lhe será perdoado.
Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
11 E, quando vos conduzirem às sinagogas, aos magistrados e potestades, não estejais solicitos de como ou do que haveis de responder nem do que haveis de falar.
“Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
12 Porque na mesma hora vos ensinará o Espírito Santo o que vos convenha falar.
gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
13 E disse-lhe um da multidão: Mestre, dize a meu irmão que reparta comigo a herança.
Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
14 Mas ele lhe disse: Homem, quem me pôs a mim por juiz ou repartidor entre vós?
Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
15 E disse-lhes: acautelai-vos e guardai-vos da avareza; porque a vida de qualquer não consiste na abundância dos bens que possui.
Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
16 E propos-lhes uma parábola, dizendo: A herdade dum homem rico tinha produzido com abundância;
Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
17 E arrazoava ele entre si, dizendo: Que farei? Não tenho onde recolher os meus frutos.
Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
18 E disse: Farei isto: Derribarei os meus celeiros, e edificarei outros maiores, e ali recolherei todas as minhas novidades e os meus bens;
“Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
19 E direi à minha alma: Alma, tens em depósito muitos bens para muitos anos: descança, come, bebe, e folga.
Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
20 Porém Deus lhe disse: Louco, esta noite te pedirão a tua alma; e o que tens preparado para quem será?
“Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
21 Assim é o que para si ajunta tesouros, e não é rico para com Deus.
“Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
22 E disse aos seus discípulos: Portanto vos digo: Não estejais solicitos pela vossa vida, no que comereis, nem pelo corpo, no que vestireis.
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
23 Mais é a vida do que o sustento, e o corpo mais do que o vestido.
Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
24 Considerai os corvos, que nem semeiam, nem segam, nem tem dispensa nem celeiro, e Deus os alimenta: quanto mais valeis vós do que as aves?
Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
25 E qual de vós, sendo solícito, pode acrescentar um côvado à sua estatura?
Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
26 Pois, se nem ainda podeis fazer as coisas mínimas, porque estais solicitos pelo mais?
Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
27 Considerai os lírios, como eles crescem; não trabalham, nem fiam; e digo-vos que nem ainda Salomão, em toda a sua glória, se vestiu como um deles.
“Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
28 E, se Deus assim veste a erva que hoje está no campo, e amanhã é lançada no forno, quanto mais a vós, homens de pouca fé?
In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
29 Vós pois não pergunteis que haveis de comer, ou que haveis de beber, e não andeis inquietos.
Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
30 Porque as gentes do mundo buscam todas essas coisas; mas vosso Pai sabe que haveis míster delas.
Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
31 Buscai antes o reino de Deus, e todas estas coisas vos serão acrescentadas.
Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
32 Não temas, ó pequeno rebanho, porque a vosso Pai agradou dar-vos o reino.
“Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
33 Vendei o que tendes, e dai esmola. Fazei para vós bolsas que não se envelheçam; tesouro nos céus que nunca acabe, aonde não chega ladrão, e a traça não roi.
Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
34 Porque, onde estiver o vosso tesouro, ali estará também o vosso coração.
Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
35 Estejam cingidos os vossos lombos, e acesas as vossas candeias.
“Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
36 E sede vós semelhantes aos homens que esperam a seu senhor, quando houver de voltar das bodas, para que, quando vier, e bater, logo possam abrir-lhe.
kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
37 Bem-aventurados aqueles servos, os quais, quando o Senhor vier, os achar vigiando! Em verdade vos digo que se cingirá, e os fará assentar à mesa, e, chegando-se, os servirá.
Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
38 E, se vier na segunda vigília, e se vier na terceira vigília, e os achar assim, bem-aventurados são os tais servos.
Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
39 Sabei, porém, isto, que, se o Pai de família soubesse a que hora, havia de vir o ladrão, vigiaria, e não deixaria minar a sua casa.
Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
40 Portanto, estai vós também apercebidos; porque virá o Filho do homem a hora que não imaginais.
Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
41 E disse-lhe Pedro: Senhor, dizes essa parábola a nós, ou também a todos?
Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
42 E disse o Senhor: Qual é pois o mordomo fiel e prudente, a quem o senhor pôs sobre os seus servos, para lhes dar a tempo a ração?
Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
43 Bem-aventurado aquele servo, o qual o senhor, quando vier, achar fazendo assim.
Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
44 Em verdade vos digo que sobre todos os seus bens o porá.
Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
45 Mas, se aquele servo disser em seu coração: O meu senhor tarda em vir; e começar a espancar os criados e criadas, e a comer, e a beber, e a embriagar-se,
Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
46 Virá o senhor daquele servo no dia em que o não espera, e numa hora que ele não sabe, e separá-lo-a, e porá a sua parte com os infieis.
Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
47 E o servo que soube a vontade do seu senhor, e não se apercebeu, nem fez conforme a sua vontade, será castigado com muitos açoites;
“Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
48 Mas o que a não soube, e fez coisas dignas de açoites, com poucos açoites será castigado. E, a qualquer que muito for dado, muito se lhe pedirá, e ao que muito se lhe confiou muito mais se lhe pedirá.
Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
49 Vim lançar fogo na terra; e que quero, se já está aceso?
“Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
50 Importa, porém, que seja batizado com um batismo; e como me angustio até que venha a cumprir-se!
Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
51 Cuidais vós que vim dar paz à terra? Não, vos digo, mas antes dissensão;
Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
52 Porque daqui em diante estarão cinco divididos numa casa: três contra dois, e dois contra três:
Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
53 O pai estará dividido contra o filho, e o filho contra o pai; a mãe contra a filha, e a filha contra a mãe; a sogra contra sua nora, e a nora contra sua sogra.
Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
54 E dizia também à multidão: Quando vêdes a nuvem que vem do ocidente, logo dizeis: Lá vem chuva, e assim sucede.
Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
55 E, quando assopra o sul, dizeis: Haverá calma; e assim sucede.
Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
56 Hipócritas, sabeis distinguir a face da terra e do céu, e como não distinguis este tempo?
Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
57 E porque não julgais também por vós mesmos o que é justo?
“Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
58 Quando pois vais com o teu adversário ao magistrado, procura livrar-te dele no caminho; para que não suceda que te conduza ao juiz, e o juiz te entregue ao meirinho, e o meirinho te encerre na prisão.
Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
59 Digo-te que não sairás dali enquanto não pagares o derradeiro ceitil.
Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”

< Lucas 12 >