< Lamentações de Jeremias 5 >

1 Lembra-te, Senhor, do que nos tem sucedido: considera, e olha o nosso opróbrio.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 A nossa herdade passou a estranhos, e as nossas casas a forasteiros.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 órfãos somos sem pai, nossas mães são como viúvas.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 A nossa água por dinheiro a bebemos, por preço vem a nossa lenha.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Padecemos perseguição sobre os nossos pescoços: estamos cançados, e nós não temos descanço.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 Aos egípcios estendemos as mãos, e aos siros, para nos fartarem de pão.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Nossos pais pecaram, e já não são: nós levamos as suas maldades.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Servos dominam sobre nós; ninguém há que nos arranque da sua mão.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 Com perigo de nossas vidas trazemos o nosso pão, por causa da espada do deserto.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Nossa pele se enegreceu como um forno, por causa do ardor da fome.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Forçaram as mulheres em Sião, as virgens nas cidades de Judá.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Os príncipes foram enforcados pelas mãos; as faces dos velhos não foram reverenciadas.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Aos mancebos tomaram para moer, e os moços tropeçaram debaixo da lenha.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 Os velhos cessaram de se assentarem à porta, os mancebos de sua canção.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Cessou o gozo de nosso coração, converteu-se em lamentação a nossa dança.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 Já caiu a coroa da nossa cabeça; ai agora de nós, porque pecamos.
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Portanto desmaiou o nosso coração, por isto se escureceram os nossos olhos.
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 Pelo monte de Sião, que está assolado, as raposas andam por ele.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Tu, Senhor, permaneces eternamente, e o teu trono de geração em geração.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Porque te esquecerias de nós para sempre? porque nos desampararias tanto tempo?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Converte-nos, Senhor, a ti, e nos converteremos: renova os nossos dias como de antes.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 Porque nos rejeitarias totalmente? te enfurecerias contra nós em tão grande maneira?
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Lamentações de Jeremias 5 >