< Juízes 10 >
1 E depois de Abimelech, se levantou, para livrar a Israel, Tola, filho de Puah, filho de Dodo, homem de Issacar: e habitava em Samir, na montanha de Ephraim.
Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
2 E julgou a Israel vinte e três anos: e morreu, e foi sepultado em Samir.
Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
3 E depois dele se levantou Jair, gileadita, e julgou a Israel vinte e dois anos.
Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
4 E tinha este trinta filhos, que cavalgavam sobre trinta jumentos; e tinham trinta cidades, a que chamaram Havoth-jair, até ao dia de hoje; as quais estão na terra de Gilead.
Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
5 E morreu Jair, e foi sepultado em Camon.
Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
6 Então tornaram os filhos de Israel a fazer o que parecia mal aos olhos do Senhor, e serviram aos baalins, e a Astaroth, e aos deuses da Síria, e aos deuses de Sidon, e aos deuses de Moab, e aos deuses dos filhos de Ammon, e aos deuses dos philisteus: e deixaram ao Senhor, e não o serviram.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
7 E a ira do Senhor se acendeu contra Israel: e vendeu-os em mão dos philisteus, e em mão dos filhos de Ammon.
sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
8 E naquele mesmo ano oprimiram e vexaram aos filhos de Israel: dezoito anos oprimiram a todos os filhos de Israel que estavam de além do Jordão, na terra dos amorreus, que está em Gilead.
waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
9 Até os filhos de Ammon passaram o Jordão, para pelejar também contra Judá, e contra Benjamin, e contra a casa de Ephraim: de maneira que Israel ficou mui angustiado.
Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
10 Então os filhos de Israel clamaram ao Senhor, dizendo: Contra ti havemos pecado, em que deixamos a nosso Deus, e em que servimos aos baalins.
Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
11 Porém o Senhor disse aos filhos de Israel: Porventura dos egípcios, e dos amorreus, e dos filhos de Ammon, e dos philisteus,
Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
12 E dos sidônios, e dos amalequitas, e dos maonitas, que vos oprimiam, quando a mim chamastes, não vos livrei eu então da sua mão?
Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
13 Contudo vós me deixastes a mim, e servistes a outros deuses: pelo que não vos livrarei mais.
Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
14 Andai, e clamai aos deuses que escolhestes: que vos livrem eles no tempo do vosso aperto.
Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
15 Mas os filhos de Israel disseram ao Senhor: pecamos, faze-nos conforme a tudo quanto te parecer bem aos teus olhos; tão somente te rogamos que nos livres neste dia.
Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
16 E tiraram os deuses alheios do meio de si, e serviram ao Senhor: então se angustiou a sua alma por causa do trabalho de Israel.
Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
17 E os filhos de Ammon se convocaram, e se puseram em campo em Gilead: e também os de Israel se congregaram, e se puseram em campo em Mispah.
Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
18 Então o povo, os príncipes de Gilead disseram uns aos outros: Quem será o varão que começará a pelejar contra os filhos de Ammon? ele será por Cabeça de todos os moradores de Gilead
Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”