< João 3 >

1 E havia entre os fariseus um homem, chamado Nicodemos, príncipe dos judeus.
Akwai wani Bafarisiye mai suna Nikodimus, wani ɗan majalisar Yahudawa.
2 Este foi ter de noite com Jesus, e disse-lhe: rabi, bem sabemos que és Mestre, vindo de Deus: porque ninguém pode fazer estes sinais que tu fazes, se Deus não for com ele.
Ya zo wurin Yesu da dad dare ya ce, “Rabbi, mun sani kai malami ne daga Allah. Gama ba wanda zai iya yin waɗannan abubuwan banmamaki da kake yi in Allah ba ya tare da shi.”
3 Jesus respondeu, e disse-lhe: Na verdade, na verdade te digo que aquele que não nascer de novo, não pode ver o reino de Deus.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an sāke haihuwarsa.”
4 Disse-lhe Nicodemos: Como pode um homem nascer, sendo velho? porventura pode tornar a entrar no ventre de sua mãe, e nascer?
Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya za a haifi mutum sa’ad da ya tsufa? Tabbatacce ba zai sāke koma sau na biyu a cikin mahaifiyarsa don a haife shi kuma ba!”
5 Jesus respondeu: Na verdade, na verdade, te digo que aquele que não nascer da água e do espírito não pode entrar no reino de Deus,
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an haife shi ta wurin ruwa da kuma Ruhu.
6 O que é nascido da carne é carne, e o que é nascido do espírito é espírito.
Jiki yakan haifi jiki, amma Ruhu yana haifi ruhu.
7 Não te maravilhes de te ter dito: necessário vos é nascer de novo.
Kada ka yi mamaki da na ce, ‘Dole ne a sāke haifarku.’
8 O vento assopra onde quer, e ouves a sua voz; porém não sabes de onde vem, nem para onde vai; assim é todo aquele que é nascido do espírito.
Iska takan hura zuwa inda take so. Kai kakan ji motsinta, sai dai ba ka iya sanin inda take fitowa ko kuwa inda za ta. Haka yake ga duk wanda aka haifa ta wurin Ruhu.”
9 Nicodemos respondeu, e disse-lhe: Como se pode fazer isto?
Nikodimus ya yi tambaya ya ce, “Yaya wannan zai yiwu?”
10 Jesus respondeu, e disse-lhe: Tu és mestre de Israel, e não sabes isto?
Yesu ya ce, “Kai ma da kake malami na Isra’ila, ba ka fahimci waɗannan abubuwa ba?
11 Na verdade, na verdade te digo que dizemos o que sabemos e testificamos o que vimos; e não aceitais o nosso testemunho.
Gaskiya nake faɗa maka, muna magana a kan abin da muka sani, muka kuma shaida abin da muka gani ne, amma har yanzu kun ƙi ku karɓi shaidarmu.
12 Se vos falei de coisas terrestres, e não crestes, como crereis, se vos falar das celestiais?
Na yi muku magana a kan abubuwan duniya amma ba ku gaskata ba; to, yaya za ku gaskata in na yi magana a kan abubuwan sama?
13 E ninguém subiu ao céu, senão o que desceu do céu, a saber, o Filho do homem, que está no céu
Ba wanda ya taɓa hawa zuwa sama sai wanda ya sauka daga sama, wato, Ɗan Mutum.
14 E, como Moisés levantou a serpente no deserto, assim importa que o Filho do homem seja levantado;
Kamar dai yadda Musa ya ɗaga maciji a hamada, haka dole ne a ɗaga Ɗan Mutum,
15 Para que todo aquele que nele crê não pereça, mas tenha a vida eterna. (aiōnios g166)
don duk mai gaskata da shi ya sami rai madawwami.” (aiōnios g166)
16 Porque Deus amou o mundo de tal maneira, que deu o seu Filho unigênito, para que todo aquele que nele crê não pereça, mas tenha a vida eterna. (aiōnios g166)
Gama Allah ya ƙaunaci duniya sosai har ya ba da wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗansa domin duk wanda ya gaskata da shi kada yă hallaka sai dai yă sami rai madawwami. (aiōnios g166)
17 Porque Deus enviou o seu Filho ao mundo, não para que condenasse o mundo, mas para que o mundo fosse salvo por ele.
Gama Allah bai aiki Ɗansa duniya don yă yi wa duniya hukunci ba, sai dai domin yă ceci duniya ta wurinsa.
18 Quem crê nele não é condenado; mas quem não crê já está condenado; porquanto não crê no nome do unigênito Filho de Deus.
Duk wanda ya gaskata da shi ba za a yi masa hukunci ba, amma duk wanda bai gaskata ba an riga an yi masa hukunci domin bai gaskata da sunan wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaicin Ɗan Allah ba.
19 E a condenação é esta: Que a luz veio ao mundo, e os homens amaram mais as trevas do que a luz, porque as suas obras eram más.
Hukuncin shi ne, Haske ya zo cikin duniya, amma mutane suka so duhu a maimakon haske domin ayyukansu mugaye ne.
20 Porque todo aquele que faz o mal aborrece a luz, e não vem para a luz, para que as suas obras não sejam arguidas.
Duk mai aikata mugunta yana ƙin haske, ba zai kuwa zo cikin haske ba don yana tsoro kada ayyukansa su tonu.
21 Mas quem obra a verdade vem para a luz, afim de que as suas obras sejam manifestas, porque são feitas em Deus.
Amma duk mai rayuwa bisa ga gaskiya yakan zo cikin haske, domin a gani a sarari cewa ayyukan da ya yi an yi su ne ta wurin Allah.
22 Depois disto foi Jesus com os seus discípulos para a terra da Judeia; e estava ali com eles, e batizava.
Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan Yahudiya, inda ya ɗan jima da su, ya kuma yi baftisma.
23 Ora João batizava também em Enon, junto a Salim, porquanto havia ali muitas águas; e vinham ali, e eram batizados.
To, Yohanna ma yana yin baftisma a Ainon kusa da Salim, saboda akwai ruwa da yawa a can, mutane kuwa suka yi ta zuwa don a yi musu baftisma.
24 Porque ainda João não tinha sido lançado na prisão.
(Wannan kuwa kafin a sa Yohanna a kurkuku.)
25 Houve pois uma questão entre os discípulos de João e os judeus, acerca da purificação.
Sai gardama ta tashi tsakanin waɗansu almajiran Yohanna da wani mutumin Yahuda a kan zancen al’adar tsarkakewa.
26 E foram ter com João, e disseram-lhe: rabi, aquele que estava contigo além do Jordão, do qual tu deste testemunho, eis que batiza, e todos vão ter com ele
Sai suka zo wurin Yohanna suka ce masa, “Rabbi, wancan mutumin da yake tare da kai a ƙetaren Urdun, wannan da ka ba da shaida a kansa sosai nan, yana baftisma, kuma kowa yana zuwa wurinsa.”
27 João respondeu, e disse: O homem não pode receber coisa alguma, se lhe não for dada do céu
Ga wannan zancen Yohanna ya amsa ya ce, “Mutum yakan karɓi kawai abin da aka ba shi ne daga sama.
28 Vós mesmos me sois testemunhas de que disse: Eu não sou o Cristo, mas sou enviado adiante dele.
Ku kanku za ku shaida cewa na ce, ‘Ba ni ne Kiristi ba, sai dai an aiko ni ne in sha gabansa.’
29 Aquele que tem a esposa é o esposo; mas o amigo do esposo, que lhe assiste e o ouve, alegra-se muito com a voz do esposo. Assim pois já este meu gozo está cumprido.
Ango ne mai amarya. Abokin da yake masa hidima yakan jira ya kuma saurara masa, yakan kuma cika da farin ciki sa’ad da ya ji muryar ango. Wannan farin cikin kuwa nawa ne, ya kuma cika a yanzu.
30 A ele convém crescer, porém a mim diminuir.
Dole ne yă yi ta ƙaruwa, ni kuma in yi ta raguwa.
31 Aquele que vem de cima é sobre todos: aquele que vem da terra é da terra e fala da terra. aquele que vem do céu é sobre todos.
“Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa; wannan da ya zo daga ƙasa na ƙasa ne, yana kuma magana kamar wanda ya zo daga ƙasa ne. Wannan da ya zo daga sama ya fi kowa.
32 E aquilo que viu e ouviu isso testifica; e ninguém aceita o seu testemunho.
Yana ba da shaidar abin da ya gani da kuma ya ji, duk da haka ba wanda ya yarda da shaidarsa.
33 Aquele que aceitou o seu testemunho, esse selou que Deus é verdadeiro.
Mutumin da ya yarda da ita ya tabbatar da cewa Allah mai gaskiya ne.
34 Porque aquele que Deus enviou fala as palavras de Deus; porque não lhe dá Deus o espírito por medida.
Gama wannan da Allah ya aiko yakan faɗi kalmomin Allah ne, gama Allah yana ba da Ruhu babu iyaka.
35 O Pai ama o Filho, e todas as coisas entregou nas suas mãos.
Uban yana ƙaunar Ɗan ya kuma danƙa kome a hannuwansa.
36 Aquele que crê no Filho tem a vida eterna; porém aquele que não crê no Filho não verá a vida; mas a ira de Deus sobre ele permanece. (aiōnios g166)
Duk wanda ya gaskata da Ɗan yana da rai madawwami, amma duk wanda ya ƙi Ɗan ba zai sami rai ba, gama fushin Allah yana nan a bisansa.” (aiōnios g166)

< João 3 >