< João 17 >
1 Jesus disse estas coisas, e levantou seus olhos ao céu, e disse: Pai, é chegada a hora; glorifica a teu Filho, para que também o teu Filho te glorifique a ti:
Bayan da Yesu ya faɗi wannan, sai ya dubi sama ya yi addu’a ya ce, “Uba, lokaci ya yi. Ka ɗaukaka Ɗanka, don Ɗanka yă ɗaukaka ka.
2 Assim como lhe deste poder sobre toda a carne, para que dê a vida eterna a todos quantos lhe deste. (aiōnios )
Gama ka ba shi iko bisa dukan mutane domin yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. (aiōnios )
3 E a vida eterna é esta: que te conheçam, a ti só, por único Deus verdadeiro, e a Jesus Cristo, a quem enviaste. (aiōnios )
Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko. (aiōnios )
4 Eu glorifiquei-te na terra, tendo consumado a obra que me deste a fazer.
Na ɗaukaka ka a duniya ta wurin gama aikin da ka ba ni.
5 E agora glorifica-me tu, ó Pai, junto de ti mesmo, com aquela glória que tinha contigo antes que o mundo existisse.
Yanzu ya Uba, ka ɗaukaka ni a gabanka da ɗaukakar da dā nake da ita tun kafin a kafa duniya.
6 Manifestei o teu nome aos homens que do mundo me deste: eram teus, e tu mos deste, e guardaram a tua palavra.
“Na bayyana ka ga waɗanda ka ba ni a duniya. Su naka ne; kai ka ba ni su sun kuma yi biyayya da maganarka.
7 Agora já tem conhecido que tudo quanto me deste vem de ti,
Yanzu sun san cewa duk abin da ka ba ni daga gare ka ya fito.
8 Porque lhes dei as palavras que tu me deste; e eles as receberam, e tem verdadeiramente conhecido que saí de ti, e creram que me enviaste.
Na ba su kalmomin da ka ba ni sun kuwa karɓa. Sun san tabbatacce daga wurinka na fito. Sun kuma gaskata kai ka aiko ni.
9 Eu rogo por eles: não rogo pelo mundo, mas por aqueles que me deste, porque são teus.
Ina addu’a dominsu. Ba domin duniya nake addu’a ba, amma domin waɗanda ka ba ni, gama su naka ne.
10 E todas as minhas coisas são tuas, e as tuas coisas são minhas; e neles sou glorificado.
Duk abin da nake da shi naka ne, kuma duk abin da kake da shi nawa ne. Na kuwa sami ɗaukaka ta wurinsu.
11 E eu já não estou mais no mundo; porém eles estão no mundo, e eu vou para ti. Pai Santo, guarda em teu nome aqueles que me deste, para que sejam um, assim como nós.
Ba sauran zamana a duniya, amma waɗannan a duniya suke, ni kuwa ina zuwa wurinka. Ya Uba Mai Tsarki, ka kiyaye su ta wurin ikon sunanka, sunan da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya.
12 Estando eu com eles no mundo, guardava-os em teu nome. Tenho guardado aqueles que tu me deste, e nenhum deles se perdeu, senão o filho da perdição, para que a escritura se cumprisse.
Yayinda nake tare da su, na kāre su na kuma kiyaye su ta wurin sunan nan da ka ba ni. Ba ko ɗayan da ya ɓace, sai dai wannan da aka ƙaddara zuwa ga hallaka don Nassi yă cika.
13 Mas agora vou para ti, e digo isto no mundo, para que tenham a minha alegria completa em si mesmos.
“Yanzu ina zuwa wurinka, sai dai na faɗi waɗannan abubuwa ne tun ina a duniya domin farin ciki yă zama cikakke a cikinsu.
14 Dei-lhes a tua palavra, e o mundo os aborreceu, porque não são do mundo, assim como eu não sou do mundo.
Na gaya musu maganarka duniya kuwa ta ƙi su, don su ba na duniya ba ne yadda ni ma ba na duniya ba ne.
15 Não rogo que os tires do mundo, mas que os livres do mal.
Ba addu’ata ba ce ka ɗauke su daga duniya ba, sai dai ka kāre su daga mugun nan.
16 Não são do mundo, como eu do mundo não sou.
Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne.
17 Santifica-os na tua verdade: a tua palavra é a verdade.
Ka tsarkake su ta wurin gaskiya; maganarka ce gaskiya.
18 Assim como tu me enviaste ao mundo, também eu os enviei ao mundo.
Kamar yadda ka aiko ni cikin duniya, haka ni ma na aike su cikin duniya.
19 E por eles me santifico a mim mesmo, para que também eles sejam santificados na verdade.
Saboda su ne na tsarkake kaina, domin su ma a tsarkake su da gaske.
20 E não rogo somente por estes, mas também por aqueles que pela sua palavra hão de crer em mim
“Addu’ata ba saboda masu bina kaɗai ba ne. Ina addu’a kuma saboda waɗanda za su gaskata da ni ta wurin maganarsu.
21 Para que todos sejam um como tu, ó Pai, em mim, e eu em ti; que também eles sejam um em nós, para que o mundo creia que tu me enviaste.
Ina so dukansu su zama ɗaya, ya Uba, kamar yadda kake a cikina, ni kuwa a cikinka. Haka su ma bari su zauna cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa kai ka aiko ni.
22 E eu dei-lhes a glória que a mim me deste, para que sejam um, como nós somos um:
Na ba su ɗaukakar da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya.
23 Eu neles, e tu em mim, para que sejam perfeitos em um, e para que o mundo conheça que tu me enviaste a mim, e que os tens amado a eles como me tens amado a mim.
Ni a cikinsu kai kuma a cikina. Bari su kasance da cikakken haɗinkai, domin duniya ta san cewa kai ka aiko ni. Ka kuwa ƙaunace su yadda ka ƙaunace ni.
24 Pai, aqueles que me deste quero que, onde eu estiver, também eles estejam comigo, para que vejam a minha glória que me deste: porque tu me as amado antes da fundação do mundo.
“Uba, ina so waɗanda ka ba ni su kasance tare da ni a inda nake, su kuma ga ɗaukakata, ɗaukakar da ka ba ni domin kana ƙaunata kafin halittar duniya.
25 Pai justo, o mundo não te conheceu; mas eu te conheci, e estes conheceram que tu me enviaste a mim.
“Ya Uba Mai Adalci, ko da yake duniya ba tă san ka ba, ni na san ka, sun kuma san kai ka aiko ni.
26 E eu lhes fiz conhecer o teu nome, e lho farei conhecer mais, para que o amor com que me tens amado neles esteja, e eu neles.
Na bayyana ka a gare su, zan kuma ci gaba da bayyana ka domin ƙaunar da ka yi mini ta kasance a cikinsu ni ma in kasance a cikinsu.”