< 8 >

1 Então respondeu Bildad o suhita, e disse:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Até quando falarás tais coisas, e as razões da tua boca serão como um vento impetuoso?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Porventura perverteria Deus o direito? e perverteria o Todo-poderoso a justiça?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 Se teus filhos pecaram contra ele, também ele os lançou na mão da sua transgressão.
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 Mas, se tu de madrugada buscares a Deus, e ao Todo-poderoso pedires misericórdia,
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 Se fores puro e reto, certamente logo despertará por ti, e restaurará a morada da tua justiça.
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 O teu princípio, na verdade, terá sido pequeno, porém o teu último estado crescerá em extremo.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 Porque, pergunta agora às gerações passadas: e prepara-te para a inquirição de seus pais
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 Porque nós somos de ontem, e nada sabemos; porquanto nossos dias sobre a terra são como a sombra.
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Porventura não te ensinarão eles, e não te falarão, e do seu coração não tirarão razões?
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Porventura sobe o junco sem lodo? ou cresce a espadana sem água?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 Estando ainda na sua verdura, ainda que a não cortem, todavia antes de qualquer outra erva se seca.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 Assim são as veredas de todos quantos se esquecem de Deus: e a esperança do hipócrita perecerá.
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 Cuja esperança fica frustrada: e a sua confiança será como a teia de aranha.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 Encostar-se-á à sua casa, mas não se terá firme: apegar-se-á a ela, mas não ficará em pé.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 Está sumarento antes que venha o sol, e os seus renovos saem sobre o seu jardim;
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 As suas raízes se entrelaçam junto à fonte, para o pedregal atenta.
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 Absorvendo-o ele do seu lugar, nega-lo-á este, dizendo: Nunca te vi?
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 Eis que este é alegria do seu caminho, e outros brotarão do pó.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 Eis que Deus não rejeitará ao reto; nem toma pela mão aos malfeitores:
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 Até que de riso te encha a boca, e os teus lábios de jubilação.
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 Teus aborrecedores se vestirão de confusão, e a tenda dos ímpios não existirá mais.
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< 8 >