< Jó 16 >
1 Então respondeu Job, e disse:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Tenho ouvido muitas coisas como estas: todos vós sois consoladores molestos.
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 Porventura não terão fim estas palavras de vento? ou que te irrita, para assim responderes?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 Falaria eu também como vós falais, se a vossa alma estivesse em lugar da minha alma? ou amontoaria palavras contra vós, e menearia contra vós a minha cabeça?
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 Antes vos fortaleceria com a minha boca, e a consolação dos meus lábios abrandaria a dor.
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 Se eu falar, a minha dor não cessa, e, calando-me eu, que mal me deixa?
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 Na verdade, agora me molestou: tu assolaste toda a minha companhia.
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 Testemunha disto é que já me fizeste enrugado, e a minha magreza já se levanta contra mim, e no meu rosto testifica contra mim.
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 Na sua ira me despedaçou, e ele me perseguiu; rangeu os seus dentes contra mim: aguça o meu adversário os seus olhos contra mim.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 Bocejam com a sua boca contra mim; com desprezo me feriram nos queixos, e contra mim se ajuntam todos.
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 Entrega-me Deus ao perverso, e nas mãos dos ímpios me faz cair.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 Descançado estava eu, porém ele me quebrantou; e pegou-me pela cerviz, e me despedaçou; também me pôs por seu alvo.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 Cercam-me os seus flecheiros; atravessa-me os rins, e não me poupa, e o meu fel derrama em terra.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 Quebranta-me com quebranto sobre quebranto: arremete contra mim como um valente.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 Cosi sobre a minha pele o saco, e revolvi a minha cabeça no pó.
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 O meu rosto todo está descorado de chorar, e sobre as minhas pálpebras está a sombra da morte:
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 Não havendo porém violência nas minhas mãos, e sendo pura a minha oração.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 Ah! terra, não cubras o meu sangue; e não haja lugar para o meu clamor!
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 Eis que também agora está a minha testemunha no céu, e a minha testemunha nas alturas.
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 Os meus amigos são os que zombam de mim; os meus olhos se desfazem em lágrimas diante de Deus.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 Ah! se se pudesse contender com Deus pelo homem, como o filho do homem pelo seu amigo!
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 Porque se passarão poucos anos; e eu seguirei o caminho por onde não tornarei.
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.