< Jeremias 40 >
1 A palavra que veio a Jeremias da parte do Senhor, depois que Nebuzaradan, capitão dos da guarda, o deixara ir de Rama, quando o tomou, estando ele atado com cadeias no meio de todos os do cativeiro de Jerusalém e de Judá, que foram levados cativos para Babilônia;
Sai magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya sake shi a Rama. Ya sami Irmiya a daure da sarƙoƙi a cikin sauran kamammu daga Urushalima da kuma Yahuda waɗanda ake kaiwa zaman bauta a Babilon.
2 Porque o capitão da guarda tomou a Jeremias, e lhe disse: O Senhor teu Deus falou este mal contra este lugar:
Sa’ad da shugaban matsaran ya sami Irmiya sai ya ce masa, “Ubangiji Allahnka ya sa wannan masifa saboda wannan wuri.
3 E o Senhor o trouxe, e fez como havia dito: porque pecastes contra o Senhor, e não obedecestes à sua voz; pelo que vos sucedeu esta coisa.
Yanzu kuma Ubangiji ya cika shi; ya yi kamar yadda ya faɗa. Dukan wannan ya faru domin kun yi zunubi ga Ubangiji ba ku kuwa yi masa biyayya ba.
4 Agora pois, eis que te soltei hoje das cadeias que estavam sobre as tuas mãos; se for bem aos teus olhos vir comigo para Babilônia, vem, e porei sobre ti os meus olhos; porém, se for mal aos teus olhos vir comigo para Babilônia, deixa de vir. Olha, toda a terra está diante de ti; para onde quer que for bom e reto aos teus olhos que vás, para ali vai.
Amma yau ina’yantar da kai daga sarƙoƙin da suke a hannuwanka. Zo mu tafi Babilon, in kana so, zan kuwa lura da kai; amma in ba ka so, kada ka zo. Ga shi, dukan ƙasar tana a gabanka; ka tafi duk inda ka so.”
5 Mas, porquanto ele ainda não tinha voltado, disse-lhe: Volta a Gedalias, filho de Ahicam, filho de Saphan, a quem o rei de Babilônia pôs sobre as cidades de Judá, e habita com ele no meio do povo; ou para qualquer parte aonde quer que for reto aos teus olhos que vás, para ali vai. E deu-lhe o capitão da guarda sustento para o caminho, e um presente, e o deixou ir.
Amma, kafin Irmiya yă juya yă tafi, Nebuzaradan ya ƙara da cewa, “Ka koma wurin Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, wanda sarkin Babilon ya naɗa a kan garuruwan Yahuda, ka zauna da shi a cikin mutane, ko kuwa ka tafi duk inda ka ga dama.” Sa’an nan shugaban ya ba shi abinci da kuma kyauta sai ya bar shi ya tafi.
6 Assim veio Jeremias a Gedalias, filho de Ahicam, a Mizpah; e habitou com ele no meio do povo que havia ficado na terra.
Saboda haka Irmiya ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa ya zauna tare da shi a cikin mutanen da aka bari a ƙasar.
7 Ouvindo pois todos os príncipes dos exércitos, que estavam no campo, eles e os seus homens, que o rei de Babilônia tinha posto sobre a terra a Gedalias, filho de Ahicam, e que lhe havia encarregado a ele os homens, e as mulheres, e os meninos, e os mais pobres da terra, os quais não foram levados cativos a Babilônia,
Sa’ad da dukan shugabannin hafsoshin tare da mutanen da suke a karkara suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya ɗan Ahikam gwamna a kan ƙasar ya kuma sa shi ya lura da maza, mata da’ya’yan da suke mafi talauci a ƙasar da waɗanda ba a kwashe zuwa zaman bauta a Babilon ba,
8 Vieram a Gedalias, a Mizpah: a saber: Ishmael, filho de Nethanias, e Johanan e Jonathan, filhos de Careah, e Seraias, filho de Tanhumeth, e os filhos de Ephai, o netophatita, e Jezanias, filho dum maachatita, eles e os seus homens.
sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan da Yonatan’ya’yan Kareya, da Serahiya ɗan Tanhumet maza,’ya’yan Efai maza, mutumin Netofa, da Yezaniya ɗan mutumin Ma’aka da mutanensu.
9 E jurou Gedalias, filho de Ahicam, filho de Saphan, a eles e aos seus homens, dizendo: Não temais servir aos caldeus: ficai na terra, e servi o rei de Babilônia, e bem vos irá.
Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, ya yi rantsuwa don yă tabbatar musu da mutanensu. Ya ce, “Kada ku ji tsoron bauta wa Babiloniyawa. Ku zauna a ƙasar ku bauta wa sarkin Babilon, zai kuma yi muku amfani.
10 Eu, porém, eis que habito em Mizpah, para estar às ordens dos caldeus que vierem a nós; e vós recolhei o vinho, e as frutas de verão, e o azeite, e metei-os nos vossos vasos, e habitai nas vossas cidades, que já tomastes.
Ni kaina zan zauna a Mizfa in zama wakilinku a gaban Babiloniyawa waɗanda za su zo wurinmu, amma ku girbe ruwan inabi,’ya’yan itatuwa na kaka, da mai, ku zuba su a tulunan ajiyarku, ku kuma zauna a garuruwan da kuka ci.”
11 Como também todos os judeus que estavam em Moab, e entre os filhos de Ammon, e em Edom, e os que havia em todas aquelas terras, ouviram que o rei de Babilônia havia deixado um resto em Judá, e que havia posto sobre eles a Gedalias, filho de Ahicam, filho de Saphan.
Sa’ad da dukan Yahudawan da suke a Mowab, Ammon, Edom da sauran ƙasashe suka ji cewa sarkin Babilon ya bar raguwa a Yahuda ya kuma naɗa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan gwamna a kansu,
12 E tornaram todos os judeus de todos os lugares, para onde foram lançados, e vieram à terra de Judá, a Gedalias, a Mizpah; e recolheram vinho e frutas do verão mui abundantes.
sai suka dawo ƙasar Yahuda, wurin Gedaliya a Mizfa, daga dukan ƙasashen da suke a warwatse. Suka girbe ruwan inabi a yalwace da’ya’yan itatuwan kaka.
13 Johanan, filho de Careah, e todos os príncipes dos exércitos, que estavam no campo, vieram a Gedalias, a Mizpah.
Yohanan ɗan Kareya da dukan manyan sojoji da suke a karkara suka zo wurin Gedaliya a Mizfa
14 E disseram-lhe: Porventura bem sabes que Baalis, rei dos filhos de Ammon, enviou a Ishmael, filho de Nethanias, para te tirar a vida. Porém não lhes deu crédito Gedalias, filho de Ahicam.
suka ce masa, “Ba ka san cewa Ba’alis sarkin Ammonawa ya aiki Ishmayel ɗan Netaniya ya ɗauke ranka ba?” Amma Gedaliya ɗan Ahikam bai gaskata su ba.
15 Todavia Johanan, filho de Careah, falou a Gedalias em segredo, em Mizpah, dizendo: Irei agora, e ferirei a Ishmael, filho de Nethanias, sem que ninguém o saiba: por que razão te tiraria ele a vida, e todo o Judá que se tem congregado a ti seria disperso, e pereceria o resto de Judá?
Sai Yohanan ɗan Kareya ya yi wa Gedaliya a Mizfa magana a asirce ya ce, “Bari in tafi in kashe Ishmayel ɗan Netaniya, ba kuwa wanda zai sani. Me zai sa ya ɗauke ranka ya watsar da dukan Yahudawan da suka taru kewaye da kai har waɗanda suka ragu na Yahuda su hallaka?”
16 Porém disse Gedalias, filho de Ahicam, a Johanan, filho de Careah: Não faças tal coisa; porque falas falso contra Ishmael.
Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohanan ɗan Kareya, “Kada ka yi irin wannan abu! Abin da kake faɗa game da Ishmayel ba gaskiya ba ne.”