< Isaías 7 >
1 Sucedeu pois nos dias de Achaz, filho de Jothão, filho d'Uzias, rei de Judá, que Resin, rei da Síria, e Peka, filho de Remalias, rei de Israel, subiram a Jerusalém, para pelejar contra ela, porém, pelejando, nada puderam contra ela.
Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
2 E deram aviso à casa de David, dizendo: A Síria repousa sobre Ephraim. Então se comoveu o seu coração, e o coração do seu povo, como se comovem as árvores do bosque com o vento
Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
3 Então disse o Senhor a Isaias: Agora tu e teu filho Sear-jasub saí ao encontro de Achaz, ao fim do canal do viveiro superior, ao caminho do campo do lavandeiro.
Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
4 E dize-lhe: Guarda-te, e está descançado, não temas, nem se desanime o teu coração por causa destes dois rabos de tições fumegantes, por causa do ardor da ira de Resin, e da Síria, e do filho de Remalias.
Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
5 Porquanto a Síria teve contra ti maligno conselho, com Ephraim, e com o filho de Remalias, dizendo:
Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
6 Vamos subir contra Judá, e despertemo-lo, e repartamo-lo entre nós, e façamos reinar no meio dele como rei o filho de Tabeal.
“Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
7 Assim diz o Senhor Deus: Isto não subsistirá, nem tão pouco acontecerá.
Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
8 Porém o cabeça da Síria será Damasco, e o cabeça de Damasco Resin: e dentro de sessenta e cinco anos Ephraim será quebrantado, e deixará de ser povo.
gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
9 Entretanto o cabeça de Ephraim será Samaria, e o cabeça de Samaria o filho de Remalias: se o não crerdes, deveras não ficareis firmes.
Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
10 E continuou o Senhor a falar com Achaz, dizendo:
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11 Pede para ti ao Senhor teu Deus um sinal; pede-o ou em baixo nas profundezas ou em cima nas alturas. (Sheol )
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol )
12 Porém disse Achaz: Não o pedirei, nem tentarei ao Senhor.
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13 Então disse: Ouvi agora, ó casa de David: Pouco vos é afadigardes os homens, senão que ainda afadigareis também ao meu Deus?
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14 Portanto o mesmo Senhor vos dará um sinal: Eis que a virgem conceberá, e parirá um filho, e chamará o seu nome Emanuel.
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15 Manteiga e mel comerá, até que ele saiba rejeitar o mal e escolher o bem.
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16 Na verdade, antes que este menino saiba rejeitar o mal e escolher o bem, a terra de que te enfadas será desamparada dos seus dois reis.
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
17 Porém o Senhor fará vir sobre ti, e sobre o teu povo, e sobre a casa de teu pai, dias tais, quais nunca vieram, desde o dia em que Ephraim se desviou de Judá, pelo rei d'Assyria.
Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
18 Porque há de acontecer que naquele dia assobiará o Senhor às moscas, que há no extremo dos rios do Egito, e às abelhas que andam na terra da Assyria;
A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
19 E virão, e pousarão todas nos vales desertos e nas fendas das penhas, e em todos os espinhos e em todas as florestas.
Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
20 Naquele dia rapará o Senhor com uma navalha alugada, que está de além do rio, com o rei da Assyria, a cabeça e os cabelos dos pés: e até a barba totalmente tirará.
A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
21 E sucederá naquele dia que alguém criará uma vaca e duas ovelhas:
A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
22 E acontecerá que por causa da abundância do leite que lhe derem comerá manteiga; e manteiga e mel comerá todo aquele que ficar de resto no meio da terra.
Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
23 Sucederá também naquele dia que todo o lugar, em que houver mil vides, do valor de mil moedas de prata, será para as sarças e para os espinheiros.
A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
24 Com arco e flechas se entrará nele, porque toda a terra será sarças e espinheiros.
Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
25 E também todos os montes, que costumam cavar com enxadas, se não irá a eles por causa do temor das sarças e dos espinheiros, porém servirão para enviarem ali bois e serem pisados do gado miúdo.
Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.