< Isaías 27 >

1 Naquele dia o Senhor castigará com a sua espada dura, grande e forte, ao Leviathan, aquela serpente comprida, e ao Leviathan, aquela serpente tortuosa, e matará o dragão, que está no mar
A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
2 Naquele dia haverá uma vinha de vinho tinto; cantai dela.
A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
3 Eu o Senhor a guardo, e cada momento a regarei; para que ninguém lhe faça dano, de noite e de dia a guardarei.
Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
4 Já não há furor em mim: quem me poria sarças e espinheiros diante de mim na guerra? eu iria contra eles e juntamente os queimaria.
Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
5 Ou pegue da minha força, e faça paz comigo: paz fará comigo.
Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
6 Dias virão em que Jacob lançará raízes, e florescerá e brotará Israel, e encherão de fruto a face do mundo
A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
7 Porventura feriu-o ele como feriu aos que o feriram? ou matou-o ele assim como matou aos que foram mortos por ele?
Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
8 Com medida contendeste com ela, quando a rejeitaste, quando a tirou com o seu vento forte, no tempo do vento leste.
Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
9 Por isso se expiará a iniquidade de Jacob, e este será todo o fruto, de se ter dado pecado: quando fizer a todas as pedras do altar como pedras de cal feitas em pedaços, então os bosques e as imagens do sol não poderão ficar em pé
A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
10 Porque a forte cidade ficará solitária, e a morada será rejeitada e desamparada como um deserto; ali pastarão os bezerros, e ali se deitarão, e devorarão as suas ramas.
Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
11 Quando as suas ramas se secarem, serão quebradas, e, vindo as mulheres, as acenderão, porque este povo não é povo de entendimento, pelo que aquele que o fez não se compadecerá dele, nem aquele que o formou lhe fará graça alguma.
Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
12 E será naquele dia que o Senhor o padejara como se padeja o trigo, desde as correntes do rio, até ao rio do Egito; e vós, ó filhos de Israel, sereis colhidos um a um
A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
13 E será naquele dia que se tocará uma grande trombeta, e os que andavam perdidos pela terra da Assyria, e os que foram desterrados para a terra do Egito tornarão a vir, e adorarão ao Senhor no monte santo em Jerusalém.
Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.

< Isaías 27 >