< Oséias 8 >
1 Põe a trombeta à tua boca; ele vem como a águia contra a casa do Senhor, porque traspassaram o meu concerto, e se rebelaram contra a minha lei.
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
2 Então a mim clamarão: Deus meu! nós, Israel, te conhecemos.
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
3 Israel rejeitou o bem: o inimigo persegui-lo-á.
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4 Eles fizeram reis, porém não de mim: constituiram príncipes, porém eu não o soube: da sua prata e do seu ouro fizeram ídolos para si, para serem destruídos.
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
5 O teu bezerro, ó Samaria, te rejeitou: a minha ira se acendeu contra eles; até quando serão eles incapazes da inocência?
Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 Porque também isso é de Israel, um artífice o fez, e não é Deus, mas em pedaços será desfeito o bezerro de Samaria.
Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
7 Porque vento semearam, e segarão tormenta: seara não haverá, a erva não dará farinha: se a der, traga-la-ão os estrangeiros.
“Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
8 Israel foi tragado: agora entre as nações será tido como um vaso em que ninguém tem prazer.
An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
9 Porque subiram à Assyria, como um jumento montez, por si só: mercou Ephraim amores.
Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
10 Ainda que eles merquem entre as nações, agora as congregarei: já começaram a ser diminuídos por causa da carga do rei dos príncipes.
Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
11 Porquanto Ephraim multiplicou os altares para pecar; teve altar para pecar.
“Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
12 Escrevi-lhe as grandezas da minha lei, porém essas são estimadas como coisa estranha.
Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
13 Quanto aos sacrifícios dos meus dons, sacrificam carne, e a comem, mas o Senhor não se deleitou neles: agora se lembrará da sua injustiça, e visitará os seus pecados: eles voltarão para o Egito.
Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
14 Porque Israel se esqueceu do seu criador, e edificou templos, e Judá multiplicou cidades fortes; mas eu enviarei um fogo contra as suas cidades, que consumirá os seus palácios.
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”