< Oséias 12 >

1 Ephraim se apascenta de vento, e segue o vento leste: todo o dia multiplica a mentira e a destruição; e fazem aliança com a Assyria, e o azeite se leva ao Egito.
Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
2 O Senhor também com Judá tem contenda, e fará visitação sobre Jacob segundo os seus caminhos; segundo as suas obras lhe recompensará.
Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
3 No ventre pegou do calcanhar de seu irmão, e pela sua força como príncipe se houve com Deus.
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4 Como príncipe se houve com o anjo, e prevaleceu; chorou, e lhe suplicou: em bethel o achou, e ali falou conosco,
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5 A saber, o Senhor, o Deus dos exércitos: o Senhor é o seu memorial.
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6 Tu, pois, converte-te a teu Deus: guarda a beneficência e o juízo, e em teu Deus espera sempre.
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
7 Na mão do mercador está uma balança enganosa; ama a opressão.
Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
8 Ainda diz Ephraim: contudo eu estou enriquecido, e tenho adquirido para mim grandes bens: em todo o meu trabalho não acharão em mim iniquidade alguma que seja pecado.
Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
9 Mas eu sou o Senhor teu Deus desde a terra do Egito: eu ainda te farei habitar em tendas, como nos dias do ajuntamento.
“Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
10 E falarei aos profetas, e multiplicarei a visão; e pelo ministério dos profetas proporei similes.
Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
11 Porventura não é Gilead iniquidade? pura vaidade são: em Gilgal sacrificam bois: os seus altares como montões de pedras são nos regos dos campos.
Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
12 Jacob fugiu para o campo da Síria, e Israel serviu por sua mulher, e por sua mulher guardou o gado.
Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
13 Mas o Senhor por um profeta fez subir a Israel do Egito, e por um profeta foi ele guardado.
Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
14 Ephraim porém mui amargosamente o irou: portanto deixará ficar sobre ele o seu sangue, e o seu Senhor lhe recompensará o seu opróbrio.
Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.

< Oséias 12 >