< Gênesis 14 >

1 E aconteceu nos dias de Amraphel, rei de Shinar, Arioch, rei de Ellasar, Chedorlaomer, rei de Elam, e Tidal, rei de Goiim,
A zamanin Amrafel sarkin Shinar, shi da Ariyok sarkin Ellasar, Kedorlayomer sarkin Elam, da kuma Tidal sarkin Goyim
2 Que estes fizeram guerra a Bera, rei de Sodoma, a Birsha, rei de Gomorra, a Shinab, rei de Admah, e a Shemeber, rei de Zeboiim, e ao rei de Bela (esta é Zoar).
suka tafi don su yaƙi Bera sarkin Sodom, Birsha sarkin Gomorra, Shinab sarkin Adma, Shemeber sarkin Zeboyim, da kuma sarkin Bela (wato, Zowar).
3 Todos estes se ajuntaram no vale de Siddim (que é o mar de sal).
Dukan waɗannan sarakuna na bayan nan suka haɗa kai a Kwarin Siddim (Teku Gishiri).
4 Doze anos haviam servido a Chedorlaomer, mas ao décimo terceiro ano rebelaram-se.
Shekara goma sha biyu suna bauta wa Kedorlayomer, amma a shekara ta sha uku sai suka yi tawaye.
5 E ao décimo quarto ano veio Chedorlaomer, e os reis que estavam com ele, e feriram aos Rephains em Ashteroth-Karnaim, e aos Zuzins em Ham, e aos Emins em Shave-kiriathaim,
A shekara ta goma sha huɗu, Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi suka tafi suka cinye Refahiyawa a Ashterot Karnayim, Zuziyawa a Ham, Emawa a Shabe Kiriyatayim,
6 E aos horeus no seu monte Seir, até à campina de Paran, que está junto ao deserto.
da Horiyawa a ƙasar tudun Seyir har zuwa El Faran kusa da hamada.
7 Lepois tornaram e vieram a Enmispat (que é Cades), e feriram toda a terra dos amalequitas, e também os amoreus, que habitavam em Hazazon-tamar.
Sa’an nan suka juya suka tafi En Mishfat (wato, Kadesh), suka cinye dukan ƙasar Amalekawa, da kuma Amoriyawa waɗanda suke zaune a Hazazon Tamar.
8 Então saiu o rei de Sodoma, e o rei de Gomorra, e o rei de Admah, e o rei de Zeboiim, e o rei de Bela (esta é Zoar), e ordenaram batalha contra eles no vale de Siddim,
Sai sarkin Sodom, sarkin Gomorra, sarkin Adma, sarkin Zeboyim da sarkin Bela (wato, Zowar), suka fita suka ja dāgā a Kwarin Siddim
9 Contra Chedorlaomer, rei de Elam, e Tidal, rei de Goiim, e Amraphel, rei de Shinar, e Arioch, rei de Ellasar; quatro reis contra cinco.
gāba da Kedorlayomer sarkin Elam, Tidal sarkin Goyim, Amrafel sarkin Shinar da Ariyok sarkin Ellasar; sarakuna huɗu gāba da biyar.
10 E o vale de Siddim estava cheio de poços de betume: e fugiram os reis de Sodoma, e de Gomorra, e cairam ali; e os restantes fugiram para um monte.
Kwarin Siddim kuwa ya cika da ramummukan kwalta, sa’ad da sarakunan Sodom da Gomorra suka gudu kuwa, waɗansu mutane suka fāɗa cikin ramummukan kwaltan, sauran kuwa suka gudu zuwa tuddai.
11 E tomaram toda a fazenda de Sodoma, e de Gomorra, e todo o seu mantimento, e foram-se.
Sarakunan nan huɗu suka washe dukan kayayyakin Sodom da Gomorra, da kuma dukan abincinsu, sa’an nan suka tafi.
12 Também tomaram a Lot, que habitava em Sodoma, filho do irmão de Abrão, e a sua fazenda, e foram-se.
Suka kuma kama Lot ɗan ɗan’uwan Abram, wanda yake zaune a Sodom, da kayayyakinsa, suka yi tafiyarsu.
13 Então veio um que escapara, e o contou a Abrão, o Hebreu: ele habitava junto dos carvalhais de Mamre, o amoreu, irmão de Eshcol, e irmão de Aner; eles eram confederados de Abrão.
Sai wani wanda ya tsira, ya zo ya faɗa wa Abram mutumin Ibraniyawa. Abram kuwa yana zama kusa da manyan itatuwan Mamre, Mamre mutumin Amoriyawa ne ɗan’uwan Eshkol da Aner, su kuwa abokan Abram ne.
14 Ouvindo pois Abrão que o seu irmão estava preso, armou os seus criados, nascidos em sua casa, trezentos e dezoito, e os perseguiu até Dan.
Da Abram ya ji cewa an kama danginsa, sai ya tara horarrun mutane 318, da aka haifa a gidansa, ya bi sawun sarakunan da suka tafi da Lot, har Dan.
15 E dividiu-se contra eles de noite, ele e os seus criados, e os feriu, e os perseguiu até Hobah, que fica à esquerda de Damasco.
Da dad dare, Abram ya rarraba mutanensa don su fāɗa wa sarakunan nan, ya ɗibge su, ya kore su har zuwa Hoba, arewa da Damaskus.
16 E tornou a trazer toda a fazenda, e tornou a trazer também a Lot, seu irmão, e a sua fazenda, e também as mulheres, e o povo.
Ya washe su da kuma dukan kayayyakinsu, ya kuma dawo da Lot danginsa da mallakarsa, tare da mata da sauran mutane.
17 E o rei de Sodoma saiu-lhe ao encontro (depois que voltou de ferir a Chedorlaomer e aos reis que estavam com ele) até ao vale de Schave, que é o vale do rei.
Bayan Abram ya dawo daga cin Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi a yaƙi, sai sarkin Sodom ya fito don yă tarye Abram a Kwarin Shabe (wato, Kwarin Sarki).
18 E Melchizedec, rei de Salém, trouxe pão e vinho: e era este sacerdote do Deus altíssimo.
Sai Melkizedek sarkin Salem ya kawo burodi da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Mafi Ɗaukaka,
19 E abençoou-o, e disse: bendito seja Abrão de Deus altíssimo, o Possuidor dos céus e da terra;
ya albarkaci Abram yana cewa, “Allah Mafi Ɗaukaka Mahaliccin sama da ƙasa yă albarkace Abram.
20 E bendito seja o Deus altíssimo, que entregou os teus inimigos nas tuas mãos. E deu-lhe o dízimo de tudo.
Kuma albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka wanda ya ba da maƙiyanka a hannunka.” Sa’an nan Abram ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome.
21 E o rei de Sodoma disse a Abrão: Dá-me a mim as almas, e a fazenda toma para ti.
Sarkin Sodom ya ce wa Abram, “Ka ba ni mutanena da ka ƙwace daga hannun sarakunan nan kawai, ka riƙe kayayyakin don kanka.”
22 Abrão, porém, disse ao rei de Sodoma: Levantei minha mão ao Senhor, o Deus altíssimo, o Possuidor dos céus e da terra,
Amma Abram ya ce, wa sarkin Sodom, “Na ɗaga hannu ga Ubangiji Allah Mafi Ɗaukaka, Mahaliccin sama da ƙasa, na riga na rantse
23 Que desde um fio até à correia de um sapato, não tomarei coisa alguma de tudo o que é teu: para que não digas: Eu enriqueci a Abrão;
cewa ba zan karɓi kome da yake naka ba, ko zare ko maɗaurin takalma, don kada ka ce, ‘Na azurta Abram.’
24 Salvo tão somente o que os mancebos comeram, e a parte que toca aos varões que comigo foram, Aner, Escol, e Mamre; estes que tomem a sua parte.
Ba zan karɓi kome ba, sai dai abin da mutanena suka ci da kuma rabon mutanen da suka tafi tare da ni, ga Aner, Eshkol, da Mamre. Bari su ɗauki rabonsu.”

< Gênesis 14 >