< Ezequiel 44 >

1 Então me fez voltar para o caminho da porta do santuário exterior, que olha para o oriente, a qual estava fechada.
Sai mutumin ya komo da ni zuwa ƙofar waje na wuri mai tsarki, wadda take fuskantar gabas, tana kuwa a rufe.
2 E disse-me o Senhor: Esta porta estará fechada, não se abrirá, nem ninguém entrará por ela; porquanto o Senhor Deus de Israel entrou por ela: por isso estará fechada.
Ubangiji ya ce mini, “Wannan ƙofar za tă kasance a rufe. Ba za a buɗe ta ba; ba wanda zai shiga ta wurinta. Za tă kasance a rufe domin Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya shiga ta wurinta.
3 O príncipe, o príncipe, ele se assentará nela, para comer o pão diante do Senhor; pelo caminho do vestíbulo da porta entrará, e pelo caminho dele sairá.
Sarki kansa ne kaɗai zai zauna a hanyar shiga don yă ci a gaban Ubangiji. Zai shiga ta hanyar shirayin hanyar shiga yă kuma fita a wannan hanya.”
4 Depois me levou pelo caminho da porta do norte, diante da casa; e olhei, e eis que a glória do Senhor encheu a casa do Senhor; então caí sobre o meu rosto.
Sa’an nan mutumin ya kawo ni ta hanyar ƙofar arewa zuwa gaban haikali. Na duba na kuma ga ɗaukakar Ubangiji tana cika haikalin Ubangiji, sai na fāɗi rubda ciki.
5 E disse-me o Senhor: Filho do homem, põe no teu coração, e olha com os teus olhos, e ouve com os teus ouvidos, tudo quanto eu falar contigo de todos os estatutos da casa do Senhor, e de todas as suas leis; e põe o teu coração na entrada da casa, com todas as saídas do santuário.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, ka lura sosai, ka saurara sosai ka kuma mai da hankali ga kome da na faɗa maka game da dukan ƙa’idodi game da haikalin Ubangiji. Ka lura sosai da ƙofar shigar haikali da kuma dukan ƙofofin wuri mai tsarki.
6 E dize ao rebelde, à casa de Israel: Assim diz o Senhor Jehovah: Bastem-vos todas as vossas abominações, ó casa de Israel!
Faɗa wa’yan tawayen gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ayyukan banƙyamarku sun isa haka, ya gidan Isra’ila!
7 Porque introduzistes estranhos, incircuncisos de coração e incircuncisos de carne, para estarem no meu santuário, para o profanarem em minha casa, quando ofereceis o meu pão, a gordura, e o sangue; e eles invalidaram o meu concerto, por causa de todas as vossas abominações.
Ban da dukan sauran ayyukanku na banƙyama, kun kawo baƙi marasa kaciya a zuciya da jiki a wurina mai tsarki, kun kuma ƙazantar da haikalina yayinda kuke miƙa mini abinci, kitse da kuma jini, kun kuma karya alkawarina.
8 E não guardastes a ordenança das minhas coisas sagradas; antes vos constituistes, a vós mesmos, guardas da minha ordenança no meu santuário.
A maimakon yin ayyukanku bisa ga abubuwana masu tsarki, kun sa waɗansu su lura da wurina mai tsarki.
9 Assim diz o Senhor Jehovah: Nenhum estranho, incircunciso de coração nem incircunciso de carne, entrará no meu santuário, dentre os estranhos que se acharem no meio dos filhos de Israel.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba baƙo marar kaciya a zuciya da jiki da zai shiga wurina mai tsarki, kai, har ma da baƙin da suke zama a cikin Isra’ila.
10 Mas os levitas que se apartaram para longe de mim, quando Israel andava errado, os quais andavam errados, desviados de mim, por irem atráz dos seus ídolos, bem levarão sobre si a sua iniquidade.
“‘Lawiyawan da suka yi nesa da ni sa’ad da Isra’ila suka kauce da kuma waɗanda suka karkata daga gare ni suka bi gumakansu, dole su ɗauki alhakin zunubinsu.
11 Contudo serão ministros no meu santuário, nos ofícios das portas da casa, e servirão a casa: eles degolarão o holocausto, e o sacrifício para o povo, e eles estarão perante eles, para os servir.
Za su iya yin hidima a wurina mai tsarki, suna lura da ƙofofin haikali suna kuma hidima a cikinsu; za su iya yankan hadayun ƙonawa da sadaka don mutane su kuma tsaya a gaban mutane su yi musu hidima.
12 Porque lhes ministraram diante dos seus ídolos, e serviram à casa de Israel de tropeço de maldade: por isso eu levantei a minha mão sobre eles, diz o Senhor Jehovah, e eles levarão sobre si a sua iniquidade.
Amma domin sun yi musu hidima a gaban gumakansu suka sa gidan Isra’ila ya yi zunubi, saboda haka na ɗaga hannu na rantse cewa dole su ɗauki alhakin zunubinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 E não se chegarão a mim, para me servirem no sacerdócio, nem para se chegarem a alguma de todas as minhas coisas sagradas, às santidades de santidades, mas levarão sobre si a sua vergonha e as suas abominações que cometeram.
Ba za su yi kusa don su yi hidima kamar firistoci ko su zo kusa da abubuwana masu tsarki ko hadayuna mafi tsarki ba; dole su sha kunya saboda ayyukansu na banƙyama.
14 Contudo, os constituirei guardas da ordenança da casa, em todo o seu serviço, e em tudo o que nela se fizer.
Duk da haka zan sa su su lura da ayyukan haikali da kuma dukan ayyukan da za a yi a cikinsa.
15 Mas os sacerdotes levíticos, os filhos de Zadoc, que guardaram a ordenança do meu santuário quando os filhos de Israel andavam errados de mim, eles se chegarão a mim, para me servirem, e estarão diante de mim, para me offerecerem a gordura e o sangue, diz o Senhor Jehovah.
“‘Amma firistoci, waɗanda suke Lawiyawa kuma zuriyar Zadok waɗanda suka yi aminci ta wurin yin ayyukansu a wurina mai tsarki sa’ad da Isra’ilawa suka kauce daga gare ni, su ne za su zo kusa don hidima a gabana; za su tsaya a gabana don miƙa hadayun kitse da jini, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
16 Eles entrarão no meu santuário, e eles se chegarão à minha mesa, para me servirem, e guardarão a minha ordenança.
Su ne kaɗai za su shiga wurina mai tsarki; su ne kaɗai za su zo kusa da teburina don yin hidima a gabana su kuma yi hidimata.
17 E será que, quando entrarem pelas portas do átrio interior, se vestirão de vestiduras de linho; e não subirá lã sobre eles, quando servirem nas portas do átrio interior, e dentro.
“‘Sa’ad da suka shiga ƙofofin fili na can ciki, dole su sa tufafin lilin; kada su sa wani rigar da aka yi da ulu yayinda suke hidima a ƙofofin fili na can ciki da cikin haikali.
18 Coifas de linho estarão sobre as suas cabeças, e ceroulas de linho estarão sobre os seus lombos: não se cingirão de modo que lhes venha suor
Za su naɗa rawunan lilin a kawunansu, su kuma sa wandunan lilin. Kada su sa wani abin da zai sa su yi zuffa.
19 E, saindo eles ao átrio exterior, ao átrio exterior ao povo, despirão as suas vestiduras com que eles ministraram, e as porão nas santas câmaras, e se vestirão de outros vestidos, para que não santifiquem o povo estando com as suas vestiduras.
Sa’ad da suka fita daga haikali zuwa fili na waje inda mutane suke, sai su tuɓe rigunan da suka yi hidima da su su bar su a tsarkakan ɗakuna, su sa waɗansu riguna, don kada su tsarkake mutane ta wurin rigunansu.
20 E a sua cabeça não raparão, nem deixarão crescer o seu cabelo; antes, como convém, tosquiarão as suas cabeças.
“‘Ba za su aske kawunansu ko su bar gashin kansu ya yi tsayi ba, amma sai su sausaye gashin kansu.
21 E nenhum sacerdote beberá vinho quando entrar no átrio interior.
Kada firist ya sha ruwan inabi sa’ad da zai shiga fili na can ciki.
22 E eles não se casarão nem com viúva nem com repudiada, mas tomarão virgens da semente da casa de Israel, ou viúva que for viúva de sacerdote.
Kada su auri gwauruwa ko macen da aka sāke; za su auri budurwai ne kaɗai na Isra’ilawa ko gwaurayen firistoci.
23 E a meu povo ensinarão a diferença entre o santo e o profano, e lhe farão saber a diferença entre o impuro e o puro.
Za su koyar da mutanena bambanci tsakanin tsarki da rashin tsarki su kuma nuna musu yadda za su bambanta marar tsarki da mai tsarki.
24 E, quando houver pleito, eles assistirão a ele para o julgarem; pelos meus juízos o julgarão: e as minhas leis e os meus estatutos em todas as minhas solenidades guardarão, e os meus sábados santificarão.
“‘A duk wani rashin jituwa, firistoci za su zama alƙalai su kuma yanke magana bisa ga farillaina. Za su kiyaye dokokina da ƙa’idodina a dukan ƙayyadaddun bukukkuwana, su kuma kiyaye Asabbataina da tsarki.
25 E eles não entrarão a homem morto, para se contaminarem; mas por pai, ou por mãe, ou por filho, ou por filha, ou por irmão, ou por irmã que não tiver marido, se poderão contaminar.
“‘Firist ba zai ƙazantar da kansa ta wurin zuwa kusa da gawa ba; amma, in gawar mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ko ɗansa ko’yarsa, ko ɗan’uwansa ko’yar’uwarsa ce, to, ba zai ƙazantar da kansa ba.
26 E, depois da sua purificação, lhe contarão sete dias.
Bayan ya tsarkaka, dole yă jira har kwana bakwai.
27 E, no dia em que ele entrar no lugar santo, no átrio interior, para ministrar no lugar santo, oferecerá a sua expiação pelo pecado, diz o Senhor Jehovah.
A ranar da ya shiga fili na can ciki na wuri mai tsarki don hidima a wuri mai tsarki, zai miƙa hadaya don zunubi saboda kansa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
28 E isto lhes será por herança: eu serei a sua herança: não lhes dareis portanto possessão em Israel: eu sou a sua possessão.
“‘Ni ne kaɗai zan zama abin gādon da firistoci za su kasance da shi. Kada ka ba su wani mallaka a Isra’ila; zan zama mallakarsu.
29 A oferta de manjares, e o sacrifício pelo pecado, e o sacrifício pela culpa eles comerão; e toda a coisa consagrada em Israel será deles.
Za su ci hadaya ta gari, hadaya don zunubi da hadaya don laifi; da kuma kowane keɓaɓɓen abu a Isra’ila da za a ba wa Ubangiji zai zama nasu.
30 E as primícias de todos os primeiros frutos de tudo, e toda a oferta de todas as vossas ofertas, serão dos sacerdotes; também as primeiras das vossas massas dareis ao sacerdote; para que faça repousar a benção sobre a tua casa.
Mafi kyau na nunan farinku da kuma dukan kyautanku na musamman za su zama na firistoci. Za ku ba su rabo na fari na ɓarzajjen hatsinku saboda albarka ta kasance a gidanku.
31 Nenhuma coisa, que de si mesmo haja morrido ou haja sido arrebatada de aves e das bestas, comerão os sacerdotes.
Firistoci ba za su ci mushen tsuntsu ko na dabba ba, ba kuwa za su ci waɗanda namun jeji suka kashe ba.

< Ezequiel 44 >